Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana
Published: 4th, August 2025 GMT
Bayanin da Hukumar Haraji ta Kasar Sin ta fitar ya nuna cewa, a rabin farko na wannan shekara, kudaden cinikin da kamfanoni a duk fadin kasar suke samu ya ci gaba da karuwa cikin kwanciyar hankali. Masana’antu sun sami ingantaccen ci gaba yayin da manufofin “sabunta manyan kayan aiki na kasa” da “Maye gurbin kayan amfani da suka tsufa da sababbi” suka yi tasiri sosai.
Kudin da aka samu a bangaren sana’ar kere-kere ya karu da sauri fiye da matsakaicin karuwar dukkan kamfanoni da kashi 1.5%.
Wannan ya tabbatar da cewa masana’antu su ne tushen karfafa tattalin arzikin kasar.
Kazalika, masana’antun kirkire-kirkire sun kara habaka, inda kudaden da aka samu a bangaren sayar da kayayyaki na masana’antun kimiyya mai inganci ya karu da kashi 14.3% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Abin da ya nuna ci gaba mai sauri a wadannan bangarori. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Yahudawa Suna Ci Gaba Da Yin Hijira Zuwa Wajen HKI
Rahotannin cibiyoyin kididdiga a HKI sun ambaci cewa, ana ci gaba da samun yin hijirar yahudwa zuwa waje wanda shi ne mafi girma a cikin shekaru da dama.
Jaridar “Ma’ariv” ta amabto wani makwararre a fagen kididdiga yana cewa; Shekarar 2024 ta fuskanci ficewar mutane masu yawan gaske daga “Isra’ila” saboda yakin da ake yi a Gaza. Haka nan kuma ya ce, wannan shi ne karo na hudu a cikin shekaru masu yawa da ake yin hijira daga Isra’ila.
Bugu da kari ya ce, baya ga yahudawa da akwai ‘yan hijira da dama da suke ficewa da hakan yake da jan hankali sosai.
Haka nan kuma ya ambaci wasu daga cikin dalilan da su ka Sanya ake yin hijira da su ka hada da rashin tsaro,da kuma tabarbarewar tattalin arziki.
A jiya Laraba ne dai cibiyar kididdiga ta ‘yan sahayoniya ta fitar da rahoto wanda ya bayyana cewa; a cikin shekarar da ta gabata kawai adadin wadanda su ka yi hijira daga “Isra’ila” sun kai 79,000.
Rahoton na jiya laraba ya kuma yi ishara da cewa; Adadin wadanda ake kira da ‘yan Isra’ila sun kai miliyan 10, da budu 148. Daga cikin wannan adadin da akwai yahudawa miliyan 7 da dubu 758, da su ne kaso 78.5 %. Su kuwa wadanda ba yahudawa ba sun kai miliyan biyu da dubu dari da talatin wato kaso 21.5%.Haka nan kuma da akwai ‘yan kasashen waje da su ka kai 260,000.Fiye da bakin haure ne su ka fice daga wannan Haramtacciyar kasa.
Kisan kiyashin da HKI ta shelanta akan Gaza ya durkusar da tattalinb arzikinta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka ‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza September 18, 2025 An Halaka Sojojin HKI Biyu Ta Hanyar Sukarsu Da Wuka A Kusa Da Iyakar Jordan September 18, 2025 Husi: Kai Wa Kasar Katar Hari Gargadi Ne Ga Al’ummar Musulmi September 18, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya bayyana Yadda Hadin Gwiwa Tsakanin Iran Da Rasha Ya Kawo Ci Gaba Tsakaninsu September 18, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai September 18, 2025 Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Masu Goyon Bayan Isra’ila Suna Da Hannu A Laifukanta September 18, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Cika Kwanaki 713 Suna Kisan Kiyashi A Zirin Gaza September 18, 2025 Harin Makami Mai Linzami Yemen Ya Tilastawa Jirgin Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Saukar Gaggawa September 18, 2025 Eslami: Dole ne IAEA ta zama mai cikakken ‘yancin cin gashin kai September 18, 2025 Rahoto: An yi tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan September 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci