Bayanin da Hukumar Haraji ta Kasar Sin ta fitar ya nuna cewa, a rabin farko na wannan shekara, kudaden cinikin da kamfanoni a duk fadin kasar suke samu ya ci gaba da karuwa cikin kwanciyar hankali. Masana’antu sun sami ingantaccen ci gaba yayin da manufofin “sabunta manyan kayan aiki na kasa” da “Maye gurbin kayan amfani da suka tsufa da sababbi” suka yi tasiri sosai.

Kudin da aka samu a bangaren sana’ar kere-kere ya karu da sauri fiye da matsakaicin karuwar dukkan kamfanoni da kashi 1.5%.

Wannan ya tabbatar da cewa masana’antu su ne tushen karfafa tattalin arzikin kasar.

Kazalika, masana’antun kirkire-kirkire sun kara habaka, inda kudaden da aka samu a bangaren sayar da kayayyaki na masana’antun kimiyya mai inganci ya karu da kashi 14.3% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Abin da ya nuna ci gaba mai sauri a wadannan bangarori. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Nijeriya (NEMA) ta ce aƙalla mutane 165 ne suka rasu, sannan 82 suka ɓace sakamakon ambaliya a bana.

NEMA ta bayyana haka ne a ranar Juma’a a wata ƙididdiga da ta fitar, tana mai cewa ambaliyar ta shafi aƙalla mutum 119,791 a bana — kuma mafi akasari mata ne da yara.

Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja

Ta bayyana cewa mutane 138 sun samu raunuka iri-iri, 43,936 sun rasa matsugunansu, gidaje 8,594 da gonaki 8,278 ne ambaliya ta shafa a cikin ƙananan hukumomi 43 da ke jihohi 19.

Ta ce, “Yara 53,314, mata 36,573, maza 24,600, tsofaffi 5,304 da kuma mutane 1,863 masu nakasa ne ambaliya ta shafa a bana.”

Jihohin da suka fi yawan waɗanda ambaliya ta shafa sun haɗa da Imo, Ribas, Abia, Borno da Kaduna.

A halin yanzu, jihohi 19 da ambaliya ta shafa sun haɗa da: Abia, Abuja, Adamawa, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Borno, Edo, Gombe, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Kogi, Kwara, Neja, Ondo, Ribas da Sakkwato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
  • WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA
  • Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
  • Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
  • Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba
  • Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya