Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-04@13:05:48 GMT

Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49

Published: 4th, August 2025 GMT

Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49

Gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana jin dadinsa kan aikin titin Eiyenkorin zuwa Afon Ojoku zuwa Offa zuwa Odo zuwa Otin mai tsawon kilomita 49 da ake ginawa.

 

Titin siminti na daya daga cikin manyan tituna hudu da ake ba da tallafi a jihar Kwara a karkashin shirin gwamnatin tarayya na karbar haraji a misalin hadakar kamfanin BUA.

 

Gwamna AbdulRazaq ya godewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa ci gaba da aiwatar da ayyukan karbar haraji da kuma sauran dimbin tallafin da yake baiwa jihar.

 

“Muna duba ayyukan titunan gwamnatin tarayya da na Jihohi, wannan sabon titin Ilorin/Offa ne, kuma za ku ga yadda yake da inganci, dole ne mu gode wa Shugaba Bola Tinubu kan wannan aikin hanyar, babban nasara ne kamar yadda kuke gani,” in ji shi.

 

A cewarsa aikin zai takaita lokacin balaguro tsakanin Ilorin, Offa da kuma makwabta. Lokacin da aka kammala hanyar, lura cewa lokacin tafiya zuwa Offa daga Ilorin zai kasance mintuna 30.

 

Gwamna AbdulRazaq ya ci gaba da cewa, wannan wani kyakkyawan jari ne kuma wani samfuri ne na ajandar sabunta fata, wanda ke nuna cewa manufofin suna aiki kuma akwai ƙarin kuɗi don samar da ababen more rayuwa.

 

A nasa jawabin injiniyan kamfanin dake aikin, Abdulsalam Onaolapo, ya ce suna aiki ba dare ba rana domin kamala aikin akan lokaci.

 

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Titi Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

“Kazalika sarkin ya bayyana cewa, mun kuma duba yanayinmu. Me muke da shi? Me za mu iya yi? Me ya kamata mu yi domin inganta rayuwar mutanenmu? Allah ya albarkaci ƙasarmu, ƙasa ce mai faɗi sosai, kuma ta dace da ayyukan noma.

Mun kuma yi la’akari da fannin ilimi. Jihar Neja, an san tana gaba a fannin ilimi. To, kwatsam, sai wannan mataki ya samu tasgaro, yara ba su iya cin jarabawar WASC, zuwa makaranta ya yi ƙasa da ƙasa, ba a kula da malamai yadda ya kamata. Wasu makarantun ba su da malamai. Za ka ga makaranta mai yawan dalibai 300 tana da malami daya ko biyu, hakan ba abu ne mai yiwuwa ba,”in ji shi.

Ya ci gaba da cewa “ɗon haka muka yanke shawarar shiga wannan fannin ilimi ta hanyar kafa makarantar firamare, sakandare, kuma Allah cikin rahamarSa, muna kafa jami’a a yanzu, wacce aka fi sani da Jami’ar Edusoko, don ƙarfafawa da kuma ci gaba da abin da gwamnati ke yi, domin mun yi imanin cewa shirye-shirye da ayyuka a cikin gwamnati ba za su iya biyan bukatun jama’a ba, kuma muna buƙatar cim ma ƙoƙarinmu.

Kazalika fannin lafiya ba mu yi sake da shi ba. Mun yanke shawarar ƙarfafa wa mutanenmu da su je neman lafiya, duba lafiyarsu a asibitoci, sannan kuma mun samu damar tattara kayan aiki don gina cibiyar kiwon lafiya inda masu ƙaramin ƙarfi za su iya zuwa. Jama’a za su je a ba su magungunan, wadanda bai da shi, mun rubuta ka je ka saya. ɗon haka, muna taimakawa a wannan ɓangare.

Sannan ya ce, “Mun gayyato wata ƙungiya mai zaman kanta, daga ƙasar Amurka, da ta zo ta yi wa jama’armu magani, masu larurar ciwon ido kyauta, da masu larurar ciwon kunne.”

da ya taɓo ɓangaren tsaro kuwa, cewa ya yi, abu ne da yake da matuƙar muhimmanci. Ku sani, shi tsaro haƙƙin kowa ne. Ganin haka ya sa muka kafa kwamitin da zai kula da harkokin tsaron cikin gida a garin Bida domin a wani lokaci mun gano cewa muna da ɗimbin matasa da ba su da aiki; wasu matasa suna shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, suna kan tituna ko kusurwoyin tituna, suna takurawa mutane, mata, musamman, da kuma mutane marasa gata. An hana fita da ƙarfe shida; dole ne ku zauna a cikin gida, in ba haka ba, za a ci zarafinku ko wani abu makamancin wannan. ɗon haka sai da muka kafa wannan kwamiti domin kula da hakan. Wannan kwamitin yana fara aiki wannan barazanar ta fara raguwa.

Batun Tsofaffin shugabanin ƙasa kuwa cewa ya yi, wadannan shugabanni da muke da su kuwa, suna da amfani gare mu, domin a yanzu suna martaba, domin wasu mutane daga wasu wurare da suke zuwa neman shawara, goyon baya da mafita ga matsalolin da suke da su. ɗon haka, sun zama abin da kuke kira gumaka, wuraren bincike, inda mutanen da ba su ma son zuwa Neja za su zo daga Arewa, Kudu, Gabas, Yamma, don ganin wadannan mutane.”

da yake magana kan dangantakarsa da sarakunan gargajiya da kuma tsofaffin sojoji kamar sarkin Musulmi, cewa ya yi, “Wannan haɗin gwiwa ce da muka samu daga sojoji mai ƙarfin gaske, hakan na motsa mu a cikin sabon aikinmu na shugabannin gargajiya da na addini.”

A ɓangaren rawar da sarakunan gargajiya ke takawa kuwa, cewa ya yi, “ Ina ganin kuskure ne a cire aikin sarakuna ko cibiyoyinsu daga kundin tsarin mulkin 1999. Kuskure ne. In ba haka ba, idan ka duba duk kundin tsarin mulkin da muke da shi, kafin samun ƴancin kai, lokacin ƴancin kai, har zuwa 1979, akwai ayyuka na cibiyoyin gargajiya.

“Amma, Allah ya san abin da ya faru, ba zato ba tsammani kwatsam an cire su. Kuma a lokacin da aka cire ɗin, akwai abin da kuke kira, taɓarɓarewar alaƙa, tsakanin gwamnati da masu mulki; an samu giɓi kuma giɓin ya yi yawa.”

Ya ci gaba cewa, “Wannan alaƙa da ta yanke. cibiyoyin gargajiya sun san abin da ake ji kuma su ne za su tilasta mutanensu sanin abin da ake so, sanin abin da suke yi, idan aka shigo da sarakuna su cikin harkokin siyasa, yanke shawara, da aiwatarwa, duk wadannan abubuwa za su yi kyau. Misali, idan za mu zauna kafada da kafada a majalisar jahohi da matakin tarayya, to manufofin ilimi, noma, kiwon lafiya da dai sauransu, idan gwamnati ta kawo abin da zai amfani al’ummarmu, to ko shakka babu za mu zartar da shi, kuma mu gamsar da al’ummarmu ba tare da tantama ba, cewa eh, wannan shirin yana da kyau a gare ku. Idan kuma gwamnati ta zo da wani abu da ba zai amfane su ba, tun daga sama a can za mu gaya wa gwamnati a’a, mutanenmu ba su saba da wannan ba, idan kuna so su yi amfani da shi, dole ne sai an bi al’adunmu na gida.”

“Wanio misalin, mu dauki batun allurar rigakafin cutar shan inna a lokaci guda, shirin ya zama wani abin tausayi, domin gwamnati ba ta sanya aikin a hannu kowa ba. ta yi gaban kanta ma’aikatanta suka tafi ƙauyuka don aiwatar da aiki, aka kore su, domin a ganinsu an zo a halaka su, a lalata musu mazaje, don haka suka nuna ba sa so. Gwamnati ta dauki lokaci mai tsawo a wannan yanayi, daga baya dole ne ta shigar da cibiyar gargajiya don shiga tsakani. Kuma a lokacin da muka shigo, mun sami damar wayar da kan jama’armu, kafin mu iya fahimtar da su ɗin, sai da muka dauki tawagar likitoci don tabbatar da gaskiyar wannan rigakafin,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, “A lokacin da muka tabbatar da cewa yana da anfani ga jama’a kuma ba ya cutar da rayuwar dan’Adam, a nan muna da ikon zuwa mu gaya wa mutanenmu, a’a, a’a, a’a, kada ku damu, wannan abu bai saɓa wa kowace lafiya ba, hasali ma zai inganta lafiyar yaranmu ne, ana nufin yara tsakanin shekara daya zuwa biyar, za a yi musu kuma za su samu lafiya. ɗon haka, mun shawo kansu. A can kuma, sun fara yarda da shirin, sannan kuma a yanzu mun yi sa’a, Majalisar ɗokoki ta 10, suna aiki ba dare ba rana, don ganin an dawo da wannan cibiya a kan turba.”

Bugu da ƙara, akwai batun, kafa cibiyoyin kiwon lafiya a dukkan ƙananan hukumominmu, 774, an kashe maƙudan kuɗi, nan ma kawai sai suka tafi ƙauyuka, don kafa cibiyoyin kai tsaye. To ka gaya min, wadanne likitocin da ke zaune a cikin birni ne za su je ƙauyukan da babu ruwa, babu haske wuta, babu ma hanyoyi kuma a ce za su yi wannan aikin?”

“da a ce an shigo da mu domin bayar da shawara, da sai mu ce a maimakon a yi dukkan ƙananan hukumomi 774, a rage su zuwa dari kacal, dari daya ko dari biyu kawai, za ku iya tsawaita su daga baya. Sannan kafin ku je ƙuyukan, ku tabbata, hanyar ƙauyen tana da kyau, ku tabbatar cewa ƙauyen yana da wutar lantarki mai amfani da hasken rana ko wani abu makamncin haka, sanna ku tabbatar akwai ruwan sha mai kyau,” in ji shi.

da ya zo batun rasuwar marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari cewa ya yi; “Mun yi imani Allah yana bayarwa kuma Allah yana karɓa, kuma dukkan rayuka daga Allah suke, kuma wajibi ne dukkan rayuka su koma gare shi. Allah ya jiƙansa, su kuma ƴan uwa na kusa, Allah ya ba su ƙwarin gwiwar jure wannan rashi mara misaltuwa, da ma al’ummar ƙasa baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa
  • Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar
  • HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja
  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
  • Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta