Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
Published: 4th, August 2025 GMT
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya bukaci sabbin mambobin hukumar yi wa kasa hidima (NYSC) da aka rantsar da su kasance masu kishin kasa da kuma ci gaba da zama ’yan kasa nagari.
Gwamna AbdulRazaq ya bayyana haka ne a yayin bikin rantsar da rukunin ‘B’, a sansanin NYSC dake Yikpata a karamar hukumar Edu.
Ya kuma shawarce su da su yi taka tsantsan wajen gudanar da ayyuka daban-daban na kwas din.
Gwamna AbdulRazaq ya tabbatar wa ‘yan yiwa kasa hidimar cewa gwamnatin jihar za ta samar da yanayin da zai taimaka musu su ci gaba.
A nasa jawabin, kodinetan NYSC na jihar, Mista Onifade Joshua, ya yabawa gwamna AbdulRazaq bisa goyon bayan da yake baiwa NYSC a jihar Kwara.
An rantsar da jimillar mambobin 1,600 da suka kunshi maza 700 da mata 900 a sansanin Yikpata.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
Tawagar Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta kai ziyarar ta’aziyya ga sabon Sarkin Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a fadarsa.
Ziyarar ta biyo bayan rasuwar marigayi Sarkin Gusau, Dakta Ibrahim Bello, wanda aka yi ta murna da shi a bisa kyakkyawan jagoranci da kuma gudunmawar ci gaban masarautu da jihar Zamfara.
Hajiya Larai Musa Lawal, ta mika sakon ta’aziyyar uwargidan shugaban kasar ga iyalan gidan sarautar tare da addu’ar Allah ya jikansa da rahama.
Ta kuma mika sakon taya murna ga sabon sarkin, tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya mai cike da hikima da zaman lafiya da hadin kai.
A nasa jawabi, sabon Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, ya nuna jin dadinsa ga uwargidan bisa wannan ziyarar da ta kai da kuma ci gaba da bada goyon baya.
Ya bayyana ta a matsayin ‘yar uwa kuma ya gode wa Gwamna Dauda Lawal bisa amincewar da aka yi masa.
Sarkin ya yi alkawarin rike gadon mahaifinsa da ya rasu tare da yin shugabanci cikin kankan da kai da sadaukarwa.
Tawagar ta kuma ziyarci Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara kuma Sarkin Anka, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad, domin yi masa ta’aziyyar rasuwar marigayi Sarkin Gusau.
Alhaji Attahiru ya yabawa uwargidan gwamnan wannan karimcin, inda ya bayyana hakan a matsayin alamar hadin kai da mutunta cibiyoyin gargajiya.
AMINU DALHATU