Mu daina zagin malaman addini idan muna son zaman lafiya — Uba Sani
Published: 5th, August 2025 GMT
Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani, ya gargadi ’yan siyasa da masu amfani da kafafen sada zumunta da su daina zagin malaman addini da a yanzu ya zama ruwan dare a ƙasar nan.
Gwamnan ya bayyana cewa irin wannan mummunar ɗabi’a ta cin zarafi malaman addini na iya lalata zamantakewa da tubalin zaman lafiya a tsakanin al’umma.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin tattaunawarsa da malaman addini da na gargajiya a birnin Kaduna, inda ya jaddada muhimmancin rawar da shugabannin addini ke takawa wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai.
Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu“Ina nanata cewa, idan muka bari shugabannin addini suka zama abin zagi da cin mutunci ba gaira ba dalili, to ita kanta ƙasar nan za ta lalace balle wata jiha. Duk lokacin da abubuwa suka rikice, wurinsu muke komawa domin neman addu’o’i,” in ji Gwamnan.
Malam Uba Sani ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu ’yan siyasa ke haɗa kai da wasu da ya bayyana da “marasa sanin abin da ya dace” wajen ɓata suna da yi wa malamai ƙage a kafafen sada zumunta.
Ya buƙaci shugabanni da mabiyansu da su guji yin amfani da malaman addini wajen biyan buƙatun siyasa ko na ƙashin kai, yana mai jaddada cewa hakan yana barazana ga zaman lafiya da jituwa da ake morewa a Kaduna da ma ƙasar baki ɗaya.
Gwamnan ya kuma yaba da rawar da malaman addini suka taka tun daga lokacin da ya hau mulki har kawo yanzu, yana cewa sun kasance ginshiƙi wajen samar da zaman lafiya a jihar.
“Da ba don su ba, da babu damar da muke da ita yau ta cin moriyar zaman lafiya a Jihar Kaduna,” in ji shi.
Ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda ’yan siyasa ke watsi da malamai bayan samun nasarar zaɓe, sannan su sake waiwayarsu idan zaɓe ya gabato.
“Muna tunawa da su ne wata ɗaya ko biyu kafin zaɓe. Muna zuwa wajen su da maganganu na yaudara da daɗin baki dangane da addini, domin su mara mana baya.”
Uba Sani ya kuma buƙaci a samar da alaƙa ta dindindin da shugabannin addini, ba sai kawai lokacin da zaɓe ya kusanto ba.
“Malamai da shugabannin addini muhimman jiga-jigai ne a tsarin ƙasa, shi ya sa muke ganin lallai muna buƙatar su a koyaushe wajen shiriya, ba sai lokacin zaɓe ba,” in ji shi.
Ya ce tun farkon mulkinsa, ya samu shawarwari masu amfani daga shugabannin addini kan batutuwan zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a jihar.
A ƙarshe, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bai wa shugabannin al’umma muhimmanci a duk wani sha’ani da ya shafi tsaro, yana mai cewa zaman lafiya mai ɗorewa ba zai samu ba sai da amincewar jama’a da haɗin gwiwa.
“Mun bayyana cewa ba za mu tura jami’an tsaro zuwa kowace unguwa ba tare da tuntubar shugabannin yankin ba. Su za su ɗauki nauyi, su tsara, sannan gwamnati ta tallafa musu,” in ji gwamnan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Rahotonni Sun Bayyana Cewa; Agajin Jin kai Da Ake Wurga Ta Sama A Gaza Tamkar Digon Ruwa Ne
Jaridar Le Monde ta bayyana cewa: Tallafin kayan da jiragen sama suke saukarwa a Gaza tamkar digon ruwa ne idan aka kwatanta girman bukatun al’ummar yankin
Jaridar Le Monde ta ruwaito cewa, ko da yake hukumomin mamayar Isra’ila, a karkashin matsin lamba na kasa da kasa, sun ba da izinin saukar da kayan agajin abinci ta hanyar jiragen sama, amma adadin tallafin takaitacce ne da ba zai magance wata matsala ba.
Le Monde ta kara da cewa: Sakamakon ya bayyana takaitacce ne a daidai lokacin da dubban manyan motoci makare da kayan agaji ke makale a wajen zirin Gaza. Jaridar ta yi bayanin cewa kasashe da dama da suka hada da Jordan, Hadaddiyar Daular Larabawa, Faransa, da Birtaniya, sun fara jigilar kayan agaji zuwa zirin Gaza mako guda da ya gabata ta hanyar amfani da jiragen yaki da ke shawagi a kan yankin Falasdinu.
Faransa za ta yi taimaka da ton 40 a jigila hudu, yayin da Spain za ta sauke tan 12. Sauran ƙasashe, kamar Belgium, Italiya, da Jamus, suma sun sanar da aniyarsu ta shiga ko ba da gudummawa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Shafa August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Bloomberg: FBI ta cire sunan Trump daga Fayilolin badakalar Epstein August 4, 2025 Jerin gwanon nuna goyon baya ga al’ummar Gaza a Sydney Australia August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci