Za a mayar da gidan yarin da ya haura shekara 100 zuwa gidan tarihi a Kano
Published: 4th, August 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta bayyana shirin mayar da tsohon gidan yarin nan na Kurmawa, wanda aka gina fiye da shekara 100 da suka gabata, zuwa gidan adana abubuwan tarihi.
Gidan yarin Kurmawa mai ɗaukar fursunoni 690 kacal, wanda aka gina a shekarar 1910 tun a zamanin Turawan mulkin mallaka a kusa da fadar mai martaba Sarkin Kano, yana da tarihin shekaru 115.
Mai ba Gwamnan Kano shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ibrahim Adam, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi.
Hadimin gwamnan ya ce an yanke shawarar sauya ma’anar wurin, daga gidan yari zuwa wuri na musamman da za a taskance abubuwan tarihi da suka shafi mulkin mallaka da kuma tarihin Jihar Kano.
A cewarsa, za a mayar da dukkan fursunonin da ke tsare a Kurmawa zuwa sabon gidan gyaran hali na zamani, wanda ke kan babbar hanyar Kano zuwa Gwarzo, a kusa da barikin sojoji da ke Janguza.
Wannan sabon gidan yari wanda aka gina shi ne a zamanin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, yana da ƙarfin ɗaukar fursunoni kusan 3,000.
Shirin na mayar da Kurmawa gidan tarihi, na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Kano na raya wuraren tarihi da al’adu, da kuma cusa wa al’umma sha’awar sanin tarihi da adana shi yadda ya kamata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidan Yari Gidan Yarin Janguza Jihar Kano Kurmawa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.
Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA