Za a mayar da gidan yarin da ya haura shekara 100 zuwa gidan tarihi a Kano
Published: 4th, August 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta bayyana shirin mayar da tsohon gidan yarin nan na Kurmawa, wanda aka gina fiye da shekara 100 da suka gabata, zuwa gidan adana abubuwan tarihi.
Gidan yarin Kurmawa mai ɗaukar fursunoni 690 kacal, wanda aka gina a shekarar 1910 tun a zamanin Turawan mulkin mallaka a kusa da fadar mai martaba Sarkin Kano, yana da tarihin shekaru 115.
Mai ba Gwamnan Kano shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ibrahim Adam, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi.
Hadimin gwamnan ya ce an yanke shawarar sauya ma’anar wurin, daga gidan yari zuwa wuri na musamman da za a taskance abubuwan tarihi da suka shafi mulkin mallaka da kuma tarihin Jihar Kano.
A cewarsa, za a mayar da dukkan fursunonin da ke tsare a Kurmawa zuwa sabon gidan gyaran hali na zamani, wanda ke kan babbar hanyar Kano zuwa Gwarzo, a kusa da barikin sojoji da ke Janguza.
Wannan sabon gidan yari wanda aka gina shi ne a zamanin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, yana da ƙarfin ɗaukar fursunoni kusan 3,000.
Shirin na mayar da Kurmawa gidan tarihi, na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Kano na raya wuraren tarihi da al’adu, da kuma cusa wa al’umma sha’awar sanin tarihi da adana shi yadda ya kamata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidan Yari Gidan Yarin Janguza Jihar Kano Kurmawa
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino
Gwamnatin Najeriya ta ce tana sa ran samun kimanin Naira biliyan 300 a duk shekara daga noman dabino a ƙasar.
Ta ce tana fatan samun wannan kuɗaɗen shiga ne daga rabon irin dabino guda miliyan biyar da ta samar ga manoma a wannan shekara ta 2025.
Darakta-Janar na Hukumar Yaƙi da Kwararowar Hamada (NAGGW), Alhaji Saleh Abubakar, ya ce, “Kowane iri ƙwaya ɗaya na iya samar da miliyan 100 na dabino, wanda kuɗinsa ya kai Naira miliyan ɗaya. Ga shi kuma sau biyu dabino ke yin ’ya’ya a shekara.
“Muna hasashen manoma za su samar da Naira biliyan 300, wanda tabbas zai bunƙasa tattalin arzikin Najeriya,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba irin dabino miliyan biyar da ta samar ga jihohi 11 da ke maƙwabtaka da saharar hamada domin su ci gajiyar tattalin arzikin noman dabino.
Ya sanar da haka ne a yayin taron ƙaddamar sashen itatuwa a ƙauyen Maimalari da ke Ƙaramar Hukumar Yusufari ta Jihar Yobe.
A cewarsa, manufar shirin ita ce bunƙasa tattalin da ke cikin ɓangaren gandun daji wajen samar da ƙarin kuɗaɗen shiga da harkokin kasuwanci a jihohi takwas da ke gaɓar hamada.