Aminiya:
2025-09-18@16:06:11 GMT

Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino

Published: 4th, August 2025 GMT

Gwamnatin Najeriya ta ce tana sa ran samun kimanin Naira biliyan 300 a duk shekara daga noman dabino a ƙasar.

Ta ce tana fatan samun wannan kuɗaɗen shiga ne daga rabon irin dabino guda miliyan biyar da ta samar ga manoma a wannan shekara ta 2025.

Darakta-Janar na Hukumar Yaƙi da Kwararowar Hamada (NAGGW), Alhaji Saleh Abubakar, ya ce, “Kowane iri ƙwaya ɗaya na iya samar da miliyan 100 na dabino, wanda kuɗinsa ya kai Naira miliyan ɗaya.

Ga shi kuma sau biyu dabino ke yin ’ya’ya a shekara.

“Muna hasashen manoma za su samar da Naira biliyan 300, wanda tabbas zai bunƙasa tattalin arzikin Najeriya,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba irin dabino miliyan biyar da ta samar ga jihohi 11 da ke maƙwabtaka da saharar hamada domin su ci gajiyar tattalin arzikin noman dabino.

Ya sanar da haka ne a yayin taron ƙaddamar sashen itatuwa a ƙauyen Maimalari da ke Ƙaramar Hukumar Yusufari ta Jihar Yobe.

A cewarsa, manufar shirin ita ce bunƙasa tattalin da ke cikin ɓangaren gandun daji wajen samar da ƙarin kuɗaɗen shiga da harkokin kasuwanci a jihohi takwas da ke gaɓar hamada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kwararowar hamada Saharar Hamada

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

 

Shugaban ya yaba da abinda ya kira kwarewa da juriya irin na Amusan, tare da cewa aikinta ya sake misalta irin daukakar da yan Nijeriya za su iya samu ta hanyar aiki tukuru da nuna kwazo, Tinubu ya yi fatan Gumel da Amusan su ci gaba da samun nasara a ayyukansu tare da ba su tabbacin gwamnati za ta ba su cikakken goyon baya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
  • Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi
  • Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa
  • ‘Yansan Jigawa Sun Tabbatarwa Mafarauta Da ‘Yan Bulala Samun Horo
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya