Aminiya:
2025-08-04@08:37:54 GMT

NAJERIYA A YAU: Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya

Published: 4th, August 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ga alama kwalliya ba ta biyan kuɗin sabulu a fafutukar da ake yi ta ganin iyaye mata sun shayar da jariransu nono zalla a wata shida na farko.

Rahotanni sun ce duk da daɗewar da aka yi ana wayar da kai har yanzu matan da suke shayar da yara nono uwa zalla ba su haura kashi 29 cikin ɗari ba.

NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi? DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suke hana mata shayar da ’ya’yansu nono zalla na watanni shida.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: nonon uwa zalla

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino

Gwamnatin Najeriya ta ce tana sa ran samun kimanin Naira biliyan 300 a duk shekara daga noman dabino a ƙasar.

Ta ce tana fatan samun wannan kuɗaɗen shiga ne daga rabon irin dabino guda miliyan biyar da ta samar ga manoma a wannan shekara ta 2025.

Darakta-Janar na Hukumar Yaƙi da Kwararowar Hamada (NAGGW), Alhaji Saleh Abubakar, ya ce, “Kowane iri ƙwaya ɗaya na iya samar da miliyan 100 na dabino, wanda kuɗinsa ya kai Naira miliyan ɗaya. Ga shi kuma sau biyu dabino ke yin ’ya’ya a shekara.

“Muna hasashen manoma za su samar da Naira biliyan 300, wanda tabbas zai bunƙasa tattalin arzikin Najeriya,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba irin dabino miliyan biyar da ta samar ga jihohi 11 da ke maƙwabtaka da saharar hamada domin su ci gajiyar tattalin arzikin noman dabino.

Ya sanar da haka ne a yayin taron ƙaddamar sashen itatuwa a ƙauyen Maimalari da ke Ƙaramar Hukumar Yusufari ta Jihar Yobe.

A cewarsa, manufar shirin ita ce bunƙasa tattalin da ke cikin ɓangaren gandun daji wajen samar da ƙarin kuɗaɗen shiga da harkokin kasuwanci a jihohi takwas da ke gaɓar hamada.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino
  • Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai 
  • Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF
  • Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi
  • Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta 
  • ’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa