NAJERIYA A YAU: Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya
Published: 4th, August 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Ga alama kwalliya ba ta biyan kuɗin sabulu a fafutukar da ake yi ta ganin iyaye mata sun shayar da jariransu nono zalla a wata shida na farko.
Rahotanni sun ce duk da daɗewar da aka yi ana wayar da kai har yanzu matan da suke shayar da yara nono uwa zalla ba su haura kashi 29 cikin ɗari ba.
Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suke hana mata shayar da ’ya’yansu nono zalla na watanni shida.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: nonon uwa zalla
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu Ta Yi Kira Ga Zaman Lafiya A Duniya
Uwargidan shugaban kasar Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira da a kara fahimtar juna a tsakanin kasashe tare da yin addu’ar samun zaman lafiya a duniya a yayin da ake fama da rikice-rikice a duniya.
Ta yi wannan kiran ne a lokacin da ta karbi bakuncin jakadan Qatar a Najeriya Ali bin Ghanem Al-Hajri a ofishinta da ke Abuja. Uwargidan shugaban kasar, yayin da take mayar da jawabi game da harin da aka kai a birnin Doha na baya-bayan nan, ta jaddada cewa, zaman lafiya, kamar yadda manyan addinai ke wa’azi, muhimmin abu ne ga bil’adama, kuma ya kamata ya kasance muhimmin fifiko ga dukkan kasashe.
Tattaunawar da aka yi a yayin ziyarar, wadda ta kasance a bayan kofofin yada labarai, ta mayar da hankali ne kan karfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyar Renewed Hope Initiative da kungiyar Qatar Foundation for Education, Science and Development Community. Bangarorin biyu sun yi nazari kan bangarorin hadin gwiwa, musamman wajen inganta tsarin karatun Almajiri da kuma tinkarar kalubalen yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya.
Ambasada Al-Hajri ya bayyana godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar da al’ummar Najeriya bisa hadin kai da kuma kiran da suke yi na samar da zaman lafiya a duniya, inda ya ce Najeriya ta kasance amintacciyar abokiyar hulda da kasar Qatar.
Bello Wakili