Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

Akalla mutane 11 ne aka kashe a harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a unguwannin Kagara da San-Isa da ke karamar hukumar Kaura-Namoda a jihar Zamfara. Majiyoyi daga yankunan biyu sun shaida wa wakilinmu cewa an kai hare-haren ne a unguwannin Kagara da San-Isa tare da wasu kauyukan da ke kewaye. Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu? Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi Wata majiya daga dan garin Kagara wanda ya bayyana sunansa da Abubakar Sani ya shaidawa LEADERSHIP cewa ya rasa ‘yan uwansa guda biyu a harin wanda ya afku a ranar Asabar din da ta gabata. Ya ce, ‘yan fashin da suka yiwa kauyen su kawanya da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Asabar, sun yi awon gaba da shanu da sauran kayayyakin mutane tare da yin garkuwa da maza da mata zuwa cikin daji. Da yake zantawa da LEADERSHIP ta wayar tarho, wani mazaunin garin, Ahmed Dan-Isa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kashe akalla mutanen kauyen 9 a ranakun Asabar da Lahadi da safe tare da yin garkuwa da wasu da dama da suka hada da maza da mata. Ahmed wanda ya ce ya tsere daga hare-haren ‘yan bindigar, amma ya ce, maharan sun mamaye kauyukan ba tare da fargabar jami’an tsaro ba. Ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta tarayya da su taimaka ta hanyar kubutar da daukacin Kaura-Namoda daga mummunan halin da take ciki. Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda (PPRO) na rundunar, Yazid Abubakar ya ci tura, domin lambar wayarsa a kashe take a lokacin hada wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
  • Kwamitin Binciken Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
  • Kwamitin Binciken Ya Kammala Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
  • Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka
  • Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu