Leadership News Hausa:
2025-06-26@23:13:04 GMT

Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu

Published: 25th, March 2025 GMT

Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu

Ba wannan tarihi na kanfar iko da ayarin farko na “yan majalisun wannan kasa ke da shi ne abin kallo ko la’akari ba, cikakkiyar dama da suke da ita a yau, tare da turbude hancin bukatun masu zabe, shi ne babban abin nadama da kaico!!!. Idan a wancan lokaci za a ce Turawa sun rike musu kugu ne, ta yadda za a ga ba su da wani tasiri ko katabus, wajen zuwa da kyawawan manufofi, don ciyar da jama’arsu gaba.

Yanzu kuwa, za a iya yi wa wadannan “yan majalisun uzuri?. Shin, suna da cikakken ikon gudanar da aiyukan nasu ko babu?. Babu shakka, duk wani irin iko da ake da bukata da tsarin mulki zai ba da, ya jima da bai wa “yan majalisun namu wannan iko ko dama a yau. To a ina ne yanzu gizo ke sakar? Cikin batutuwan da za a bijirar gaba, a nan ne kowa ke da ikon yin tsifa game da gurbacewar al’amuran majalisa a Nijeriyar yau.

“…The composition and functioning of the legislatibe council, howeber, pointed to the fact that, it was nothing more than a mere rubber-stamping institution…”.

(Fagge & Alabi, 2007: 5b).

Wadancan kalamai na sama cikin harshen Turanci, na yin nuni ne da cewa, “yan majalisun Nijeriya a wancan lokaci da Turawan Birtaniya ke mulkarmu, ba su kasance komai ba, face “yan-abi-yarima ne cikin harkokin zaman majalisar. Duk abinda aka yanke a majalisar, kawai sai dai su sanya-hannu ne akai. Ba su da ikon tabbatar da wani kudiri, koko yin watsi da shi. Tun da, hatta mafi yawan adadin mutanen da ke cikin zauren na majalisar, za a samu cewa, gwamna ne ya zabe su da hannunsa, kamar yadda a rubutun baya aka faiyace irin adadinsu dalla-dalla.

Batun rashin iko, ko karancinsa, shi ne babban abinda ya mamaye harkokin “yan majalisun na kasa gabanin Nijeriya ta kai ga samun “yancin-kai. Sai dai, a kan samu wasu “yan canje-canje ne daga lokaci zuwa lokaci, sakamakon mabanbantan kundin tsarin mulkin da Turawan suka gabatar mana da su gabanin kai wa ga samun yancin-kai. Tulin labaran “yan majalisun na da auki ainun, kawai za mu yi kokarin matsawa gaba ne cikin hanzari, don kai wa ga yadda lamuran majalisar ke wakana a yau, wanda shi ne babban abinda muke son yin doguwar tattaunawa akai sannu a hankali.

 

“Yan Majalisunmu A Shekarar 1900

Ya tabbata, bayan samun “yancin-kai a wannan Kasa (cikin Shekarar 19b0), “yan majalisun namu, sun kai ga fara samun “yancin gudanar da aiyukansu, sama da irin yadda suka kasance a baya. Tsarin mulki irin na shugaban kasa daban, da shugaban gwamnati (tsarin mulkin firaminista) daban, aka fara dabbakawa a wannan kasa bayan samun mulkin kai. A karkashin tsarin mulkin, za a ga irin aikace-aikacen da wadannan ‘yan majalisun namu na lokacin suka gudanar, kafin juyin mulkin Soja na farko da aka fara yi a kasar, cikin Shekarar 19bb, Shekaru shida (b) kacal, bayan samun yancin-kai. Ke nan, irin ayyukan da suka gudanar cikin majalisar, zai zamto ne a tsakanin Shekarar 1900 da Shekarar 1900.

Ga wasu daga irin ayyukan da bangaren “yan majalisun suka gudanar kamar haka;

i- Kafa Gwamnati: “yan majalisun ne suka taka rawa wajen zabar firaminista Abubakar Tafawa Balewa a matsayin shugaban gwamnati, tare da yunkurin fasalta tsarin gwamnatin dimukradiyya.

ii- Ci gaban bangaren dokoki: “yan majalisun, sun samar da dokoki kyawawa, musamman wadanda suka shafi ci gaban tattalin arzikin kasa, ilimi tare da samun cikakken ikon gudanarwa a cikin lardunan kasar da ake da su.

iii- Kyautata Wakilci A Gwamnatin Hadaka Da Na Larduna: tsarin, ya ba da dama ga jagororin gwamnati (firimiyoyi) na lardunan arewa da yamma da na gabashin kasar, na su shigo cikin lamuran gudanar gwamnati dumu-dumu, don a dama da su.

ib- Canjin Mirginawar Tsarin Mulki Na Kasa: “yan majalisun, sun taka rawa muhimmiya, wajen dawowar tsarin mulkin dake nuna lamuran Kasar, na gudana karkashin ikon Sarauniyar Birtaniya ne, zuwa ga wata jamhuriya mai zaman kanta cikin Shekarar 19b3, wadda ikonta ya sabbawa Dr Nnamdi Azikiwe zama shugaban kasar Nijeriya na farko.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan majalisun na tsarin mulkin

এছাড়াও পড়ুন:

An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta gabatar da cakin kuɗi Naira 13 da dubu ɗari 4 da 28 da ɗari 6 da 59.95 ga ’yan uwan ​​’yan sanda 10 da suka mutu a bakin aiki.

Taron gabatar da kuɗin wanda aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Maiduguri, na da nufin bayar da tallafin kuɗi ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana hakan ne manema labarai a hedikwatar rundunar da ke garin Maiduguri.

Kwamishinan ’yan sanda, CP Naziru Abdulmajid ne ya gabatar da jawabin a madadin Sufeto-Janar na ’yan sanda (IGP), Kayode Adeolu Egbetokun.

Wannan shiri yana ƙarƙashin Ƙungiyar ’yan sandan Najeriya (Group Assurance Life and IGP Welfare Scheme) wanda aka tsara don rage wahalhalun da iyalan ma’aikatan da suka yi sadaukarwa ke fuskanta.

Kwamishina Abdulmajid ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasu, yana mai tabbatar musu da jajircewar sufeto-janar na ’yan sanda na tabbatar da jin daɗin jami’an da ke aiki da kuma jaruman da suka mutu.

Ya jaddada cewa, sadaukarwar da waɗannan jami’an suka yi ba za a taɓa mantawa da su ba, kuma rundunar ta ci gaba cewa za ta ci gaba sadaukar da kai wajen tabbatar da jin daɗin iyalan da suka bari.”

Kwamishinan ’yan sandan ya kuma shawarci waɗanda suka ci gajiyar kuɗaɗen da su yi amfani da kuɗaɗen cikin adalci, inda ya buƙace su da su saka hannun jari a harkar kasuwanci mai ɗorewa da zai taimaka wajen tabbatar da makomar waɗanda suka mutu na jami’an na su.

Da yake jawabi a madadin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Jerry Joel ya bayyana matuƙar godiya ga rundunar ’yan sandan Najeriya da babban sufeton ’yan sandan ƙasar bisa goyon bayan da suka bayar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale a gare su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
  • Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
  • NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3