Aminiya:
2025-11-04@07:32:07 GMT

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami

Published: 5th, August 2025 GMT

Tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ba wa ɗalibar nan ’yar shekara 17 daga Jihar Yobe da ta lashe Gasar Turanci ta Duniya, Nafisa Abdullah Aminu, kyautar tsabar kuɗi Dala 100,000 da gida da kuma lambar girmamawa ta OON.

Ya buƙaci a gayyato Nafisa da malamanta na harshen Turanci musamman zuwa Fadar Shugaban Ƙasa a karrama su saboda yadda suka ɗaga sunan Najeriya a idon duniya a fannin ilimi.

“Ina kira da babbar murya cewa a a ba wa Nafisa kyautar tsabar kuɗi Dala 100,000 da gida da kuma lambar girmamawa daga Gwamnatin Tarayya.”

A cikin saƙon da ya wallafa a safiyar Talata, Pantami ya ƙara da cewa malaman Nafisa sun cancanci irin kyautar da aka yi wa tawagar masu horas da ’yan wasan Najeriya ta lambar OON da tsabar kuɗi Dala 50,0000 da kuma gida ga kowannensu, musamman ma tun da nasarar da suka samu a fannin ilimi ne.

’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje

“Su ma malananta a ba su kyauta irin wadda aka yi wa masu horas da ’yan wasan ƙwallon Najeriya. Wajibi ne mu ba wa ilimi muhimmancin da ya dace tare da karrama ƙwazon ’yan kasarmu,” in ji Pantami.

Bayanin na zuwa ne washegarin da Gwamnatin Tarayya ta yi irin wannan kyauta ga kowacce daga ’yan wasan ƙwallon kwandon Najeriya na D’Tigress kan lashe gasar Kaifin Nahiyar Afirka ta shekarar 2025.

Ƙasa da mako guda ke nan kuma bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi irin wannan kyauta ga ’yan wasan ƙwallon ƙafan mata ta Super Falcons bayan sun lashe gasar Kofin Nahiyar Afirka ta bana.

Aminiya ta ruwaito cewar Nafisa Abdullah Aminu ta lashe Gasar Turanci ta Duniya ta Teen Eagle da aka gudanar a ƙasar Birtaniya.

Nafisa daga Kwalejin Nigeria Tulip International (NTIC) da ke Jihar  Yobe ta doke abokan fafatawarta daga ƙasashe 69 domin zama Gwarzuwar Shekarar 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Turanci kyautar Dala 100 yan wasan ƙwallon

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”

Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”

Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.

“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.

Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.

Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.

Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.

“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.

“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa November 1, 2025 Manyan Labarai Jerin Gwarazan Taurarinmu November 1, 2025 Manyan Labarai Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sinner da Alcaraz za su buga wasan baje koli a Koriya ta Kudu
  • Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3