WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025
Published: 4th, August 2025 GMT
Hukumar da ke shirya jarabawa kammala karatun sakandire a Afrika ta Yamma (WAEC), ta saki sakamakon jarabawar SSCE na shekarar 2025.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Litinin, 4 ga Agustan 2025, tana mai cewa dukkan ɗaliban da suka zauna jarabawar yanzu za su iya duba sakamakon nasu a shafinta na intanet.
“WAEC na farin cikin sanar da ɗalibai da suka rubuta jarabawar WASSCE a shekarar 2025 cewa an saki sakamakon a hukumance yau Litinin, 4 ga watan Agusta,” in ji sanarwar.
WAEC ta buƙaci ɗalibai da su shiga shafin duba sakamako na hukuma a (http://waecdirect.org) ko (http://waecdirect.org) domin duba sakamakon su ta amfani da bayanan jarabawa da lambobin tantance sakamako wato result checker pins.
A nasa bangaren, shugaban ofishin WAEC na Nijeriya, Amos Dangut, ya bayyana cewa an samu raguwar kashi 33.8 cikin ɗari na sakamako masu kyau idan aka kwatanta da na shekarar 2024.
Da yake zantawa da manema labarai a birnin Legas, Dangut ya ce kashi 72.12 cikin ɗari na ɗaliban da suka samu makin credit ko fiye aƙalla darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi — adadi ne da ya yi kasa da na bara da kusan kashi 34 cikin ɗari.
“A ƙididdigar da muka yi tsakanin sakamakon jarabawar 2024 da na 2025, mun lura cewa an samu raguwar kashi 33.8 cikin ɗari a yawan ɗaliban da suka samu makin credit ko fiye a aƙalla darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi,” in ji shi.
Aminiya ta rawaito cewa wannan dai na zuwa ne bayan ɗalibai da iyaye da su kansu makarantun sakandare a faɗin ƙasar sun shafe makonni suna dakon fitowar sakamakon jarabawar na bana.
Jimillar ɗalibai 1,973,253 daga makarantu 23,554 da aka amince da su ne suka zauna jarabawar bana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jarabawa WAEC sakamakon jarabawar cikin ɗari
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria