Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Namijin Kokarinsu
Published: 4th, August 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun dakile shirin ‘yan sahayoniyya a yakin kwanaki 12
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Al’ummar Iran sun dakile shirin yahudawan sahayoniyya a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa. A lokacin da yake halartar taron manema labarai da kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Ismail Baqa’i ya gudanar a yau Litinin, Araqchi ya ce: Na farko dai ya zama wajibi a gare shi ya girmama dukkanin shahidai: shahidan juyin juya halin Musulunci, shahidan tsaro mai alfarma (1980-1988), da dukkanin shahidan da suka sadaukar da rayuwarsu wajenkare kasa, tun farko-farko har zuwa yau, musamman ‘yan jaridu da shahida yakin matsorata masu wuce gona da iri na yakin kwanaki 12.
Ministan harkokin wajen kasar ya kara da cewa: Babu shakka wannan yaki zai kasance daya daga cikin abubuwan da ba za a taba mantawa da shi ba a tarihin Iran na yau da kullum, yakin da gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu laifi tare da goyon baya da hadin gwiwar manyan kasashen duniya da sauran su suka kaddamar na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da fatan cimma munanan manufofinsu da wani harin ba-zata cikin kankanin lokaci, to sai dai al’ummar Iran sun sake tabbatar cewa sun yi tsayin daka tare da zage dantse babu abin da zai kawar da su kan azamarsu, saboda mutane suna ne da saiwoyinsu suka shimfiɗa a cikin kasa sama da dubban shekaru, saiwoyin suke kara karfi kowace rana, ƙasar da ta wanzu saboda sadaukarwa, da tsayin daka, da Imani.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin August 4, 2025 Rahotonni Sun Bayyana Cewa; Agajin Jin kai Da Ake Wurga Ta Sama A Gaza Tamkar Digon Ruwa Ne August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Shafa August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Ministan harkokin wajen kasar Al ummar Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
Kasashen Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan hadin kan Musulmi game da halin da ake ci a yankin
Wannan bayannin ya fito ne a yayin ganawar sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani da yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya Mohammed bin Salman a birnin Riyadh inda suka tattauna kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma halin da ake ciki a yankin.
Ganawar dai ta nuna wani muhimmin mataki a huldar diflomasiyya ta tsakanin Tehran da Riyadh.
Larijani ya tafi Saudiyya ne bisa gayyatar da ministan tsaron kasar ya yi masa, inda ya jagoranci tawagar da ta hada da mataimakin sakataren harkokin kasa da kasa Ali Bagheri Kani da mai ba da shawara kan harkokin yankin Gulf na Farisa Mohammad Ali Bek.
Ganawar na zuwa ne kwana guda kacal bayan da shugaba Masoud Pezeshkian ya gana da bin Salman a gefen taron gaggawa na kasashen Larabawa da Musulunci da aka yi a birnin Doha, inda bangarorin biyu suka nuna gamsuwarsu da yadda huldar dake tsakanin kasashen biyu ke kara habaka.
Ziyarar Larijani a Riyadh ita ce ziyararsa ta uku a yankin tun bayan hawansa mulki a ranar 5 ga watan Agusta, biyo bayan ziyarar da ya kai a Iraki da Lebanon.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci