Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi gargaɗin cewa za a yi ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da tsawa na kwaki uku a faɗin ƙasar daga ranar Litinin.

NiMet ta fitar da wannan hasashen ne ranar Lahadi a Abuja, lamarin da ke ƙara barazanar ambaliya a wasu jihohin ƙasar.

Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino

Hasashen na zuwa ne bayan ruwan sama ya lalata gidaje kimanin 50 da gonaki da wuraren ibada a Jihar Filato.

Hukumar ta yi hasashen cewa za a yi tsawa da ruwan sama a jihohin arewacin ƙasar da suka haɗa da Adamawa da Taraba da Sakkwato da Kebbi da Zamfara da Jigawa da Kano da kuma Katsina ranar Litinin, kuma lamarin zai yi ƙamari zuwa yammacin ranar.

“Akwai yiwuwar samun ambaliya a wasu sassan jihohin Adamawa da Taraba da kuma Bauchi a wannan lokacin da aka yi hasashen,” kamar yadda NiMet ta bayyana a sanarwar.

A tsakiyar Nijeriya, ana sa ran saukar ruwan sama kaɗan da safiya a jihohin Binuwai da Neja da Kogi da Nasarawa da Kuma Birnin Tarayya Abuja.

Kuma zuwa rana da yamma, ana sa ran ruwan saman zai kai jihohin Filato da Kwara da kuma sauran jihohi maƙwabta.

A yawancin jihohin kudancin ƙasar dai hasashen hadari ake yi, inda ake ganin yiwuwar samun ruwan sama kaɗan a jihohin Ebonyi da Enugu da Imo da Anambra da Abia da Ogun da Edo da Delta da Legos da Ribas da Cross Rivers da Akwa Ibom da kuma Bayelsa da sanyina safiya.

Amma daga baya ana sa rai za a yi ruwa mai yawa, inda NiMet ke gargaɗin cewa za a iya samun ambaliya a jihohin Oyo da Ogun da Edo da kuma Delta.

Ranar Talata, hukumar tana hasashen cewa za a ci gaba da samun ruwan sama mai yawa da tsawa a yankin arewacin ƙasar musamman a jihohin Taraba da Katsina da Kebbi da Sokoto da Kaduna da kuma Zamfara.

“Ana tsammanin matsakaicin ruwan sama da tsawa a faɗin yankin daga baya a ranar,” in ji hukumar.

Jihohin tsakiyar ƙasar ciki har da Abuja, na tsammanin ruwan sama mai ɗaukewa da dawowa, yayin da jihohin kudancin ƙasar daga Legas zuwa birnin Calabar za su iya fuskantar ruwan sama babu ƙaƙƙautawa.

NiMet ta ja hankalin mazauna jihohin Anambra da Delta da Bayelsa da Cross River da kuma Akwa Ibom su shirya wa yiwuwar ambaliya.

Zuwa ranar Laraba, ana sa ran ruwan sama da tsawa zai karaɗe jihohin Taraba da Kaduna cikin sanyin safiya, inda kuma za a samu guguwa da ruwan sama daga baya a jihohin Borno da Bauchi da Gombe da Jigawa da kuma Kano.

Yankin tsakiyar ƙasar kuma zai sake ganin yayyafi da safiya, kuma da rana za a yi ruwan sama mai yawa.

A kudanci kuwa, ana hasashen za a yi ruwan sama mai ɗaukewa da dawowa a jihohin Legas da Ribas da Bayelsa da Cross River. Jihar Bayelsa ta fi fuskantar barazanar ambaliya a tsakiyar mako, in ji hukumar

Hukumar ta yi kira ga mazauna jihohin su ɗauki matakan kauce wa barazanar ambaliyar.

“[Ku] kaurace wa tuƙi a cikin ruwan sama mai ƙarfi, kuma jihohin da ke da yiwuwar samun ambaliya su yi tsare-tsarensu na ba da agajin gaggawa nan-take,” in ji hasashen.

NiMet ta kuma shawarci magidanta su ɗaure ababen da ka iya faɗuwa kuma su sanya rigunan sanyi tare da cire kayan laturoni daga lantarki a lokacin guguwa.

Hukumar ta kuma shawarci kamfanonin jiragen sama su nemi shawarwari na yanayi wajen shirya jadawalin jigilar matafiyansu.

NiMet ta buƙaci ‘yan Nijeriya su bibiyi shafinta na intanet don samun ƙarin bayani kan yanayi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Hasashen Yanayi ruwan sama ruwan sama mai

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Cika Kwanaki 713 Suna Kisan Kiyashi A Zirin Gaza

Gwamnatin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare kan Gaza a rana ta 713 a daidai lokacin da kasashen duniya ke shiru

Sojojin mamayar Isra’ila sun ci gaba da yakin kisan kare dangi a zirin Gaza a rana ta 713, inda suke ci gaba da yin amfani da ruwan bama-bamai ta sama da na bindigogi, inda suka kashe mutane da ke fama da yunwa da rashin muhallan, tare da goyon bayan siyasa da soji na Amurka, gami da shirun kasa da kasa, da gazawar da ba a taba gani ba daga kasashen duniya.

Sojojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-hare da dama ta sama tare da aiwatar da kisan kiyashi, lamarin da ya ta’azzara wahalhalun da mutane sama da miliyan biyu suka rasa muhallansu ga kuma bullar masifar tsananin yunwa. Hare-haren wuce gona da iri kan birnin Gaza ya kara tsananta da nufin raba su da mazaunansu da kuma rusa yankin baki daya.

Majiyoyin lafiya a asibitocin Gaza sun tabbatar da mutuwar wasu Falasdinawa da dama da sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka harba tun daga wayewar garin ranar alhamis, musamman a birnin Gaza, inda rikicin yunwa da barna ke kara ta’azzara yayin da sojojin mamayar Isra’ilaa ke neman korar mazaunanta gaba daya.

Asibitin Al-Awda da ke birnin Nuseirat ya bayar da rahoton cewa, a daren jiya ya karbi shahidai hudu tare da jikkata wasu 10, sakamakon harin da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida da ke Block 7 na sansanin ‘yan gudun hijira na Al-Bureij da ke tsakiyar zirin Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Harin Makami Mai Linzami Yemen Ya Tilastawa Jirgin Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Saukar Gaggawa September 18, 2025 Eslami: Dole ne IAEA ta zama mai cikakken ‘yancin cin gashin kai September 18, 2025 Rahoto: An yi tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan September 18, 2025 Sheikh Qassem: Harin Pager jarabawa ce wadda ta kara wa masu gwagwarmaya kwarin gwiwa September 18, 2025 Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya September 18, 2025 Iran ta samu Zinariya, Azurfa, da Tagulla a Gasar Kokawa ta Duniya September 18, 2025 Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam Da Zai Samar Da “Internet” Ga Yankunan Karkara September 17, 2025 Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea September 17, 2025 Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro September 17, 2025 Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar Kasuwanci Da HKI September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Cika Kwanaki 713 Suna Kisan Kiyashi A Zirin Gaza
  • Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
  • Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara