Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi gargaɗin cewa za a yi ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da tsawa na kwaki uku a faɗin ƙasar daga ranar Litinin.

NiMet ta fitar da wannan hasashen ne ranar Lahadi a Abuja, lamarin da ke ƙara barazanar ambaliya a wasu jihohin ƙasar.

Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino

Hasashen na zuwa ne bayan ruwan sama ya lalata gidaje kimanin 50 da gonaki da wuraren ibada a Jihar Filato.

Hukumar ta yi hasashen cewa za a yi tsawa da ruwan sama a jihohin arewacin ƙasar da suka haɗa da Adamawa da Taraba da Sakkwato da Kebbi da Zamfara da Jigawa da Kano da kuma Katsina ranar Litinin, kuma lamarin zai yi ƙamari zuwa yammacin ranar.

“Akwai yiwuwar samun ambaliya a wasu sassan jihohin Adamawa da Taraba da kuma Bauchi a wannan lokacin da aka yi hasashen,” kamar yadda NiMet ta bayyana a sanarwar.

A tsakiyar Nijeriya, ana sa ran saukar ruwan sama kaɗan da safiya a jihohin Binuwai da Neja da Kogi da Nasarawa da Kuma Birnin Tarayya Abuja.

Kuma zuwa rana da yamma, ana sa ran ruwan saman zai kai jihohin Filato da Kwara da kuma sauran jihohi maƙwabta.

A yawancin jihohin kudancin ƙasar dai hasashen hadari ake yi, inda ake ganin yiwuwar samun ruwan sama kaɗan a jihohin Ebonyi da Enugu da Imo da Anambra da Abia da Ogun da Edo da Delta da Legos da Ribas da Cross Rivers da Akwa Ibom da kuma Bayelsa da sanyina safiya.

Amma daga baya ana sa rai za a yi ruwa mai yawa, inda NiMet ke gargaɗin cewa za a iya samun ambaliya a jihohin Oyo da Ogun da Edo da kuma Delta.

Ranar Talata, hukumar tana hasashen cewa za a ci gaba da samun ruwan sama mai yawa da tsawa a yankin arewacin ƙasar musamman a jihohin Taraba da Katsina da Kebbi da Sokoto da Kaduna da kuma Zamfara.

“Ana tsammanin matsakaicin ruwan sama da tsawa a faɗin yankin daga baya a ranar,” in ji hukumar.

Jihohin tsakiyar ƙasar ciki har da Abuja, na tsammanin ruwan sama mai ɗaukewa da dawowa, yayin da jihohin kudancin ƙasar daga Legas zuwa birnin Calabar za su iya fuskantar ruwan sama babu ƙaƙƙautawa.

NiMet ta ja hankalin mazauna jihohin Anambra da Delta da Bayelsa da Cross River da kuma Akwa Ibom su shirya wa yiwuwar ambaliya.

Zuwa ranar Laraba, ana sa ran ruwan sama da tsawa zai karaɗe jihohin Taraba da Kaduna cikin sanyin safiya, inda kuma za a samu guguwa da ruwan sama daga baya a jihohin Borno da Bauchi da Gombe da Jigawa da kuma Kano.

Yankin tsakiyar ƙasar kuma zai sake ganin yayyafi da safiya, kuma da rana za a yi ruwan sama mai yawa.

A kudanci kuwa, ana hasashen za a yi ruwan sama mai ɗaukewa da dawowa a jihohin Legas da Ribas da Bayelsa da Cross River. Jihar Bayelsa ta fi fuskantar barazanar ambaliya a tsakiyar mako, in ji hukumar

Hukumar ta yi kira ga mazauna jihohin su ɗauki matakan kauce wa barazanar ambaliyar.

“[Ku] kaurace wa tuƙi a cikin ruwan sama mai ƙarfi, kuma jihohin da ke da yiwuwar samun ambaliya su yi tsare-tsarensu na ba da agajin gaggawa nan-take,” in ji hasashen.

NiMet ta kuma shawarci magidanta su ɗaure ababen da ka iya faɗuwa kuma su sanya rigunan sanyi tare da cire kayan laturoni daga lantarki a lokacin guguwa.

Hukumar ta kuma shawarci kamfanonin jiragen sama su nemi shawarwari na yanayi wajen shirya jadawalin jigilar matafiyansu.

NiMet ta buƙaci ‘yan Nijeriya su bibiyi shafinta na intanet don samun ƙarin bayani kan yanayi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Hasashen Yanayi ruwan sama ruwan sama mai

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

Fadar Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa nan da wasu kwanaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gana da takwaransa na Amurka, Donald Trump, domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya.

Mai ba wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, ne ya tabbatar da hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan

A cewar Daniel Bwala, shugabannin biyu — Tinubu da Trump — sun yi tarayya da juna kan fahimta ta haɗin kai wajen yaƙi da ta’addanci da duk wata barazana ga bil’adama.

“A bayan nan Shugaba Trump ya taimaka wajen ba da izinin sayar wa Nijeriya makamai, kuma Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar yadda ya kamata wajen yaƙi da ta’addanci, kuma muna da sakamakon da za mu iya nunawa,” in ji Bwala.

Ya ƙara da cewa duk wani saɓanin fahimta kan ko ‘yan ta’adda a Nijeriya na kai hari ne ga Kiristoci kaɗai ko kuma mabiyan addinai daban-daban, “za a tattauna kuma a warware su” a yayin ganawar shugabannin biyu, wadda za ta gudana “ko dai a Fadar Shugaban Kasa ta Abuja, ko a Fadar White House da ke Washington.”

Sanarwar ta zo ne bayan barazanar Shugaba Trump ta kai farmaki a Nijeriya, inda ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta fara tsara yadda za a kai hari kan ƙasar, saboda abin da ya kira “kisan gillar da ake yi wa Kiristoci” a Nijeriya.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, Trump ya ce Amurka “a shirye take ta turo sojojinta da manyan makamai zuwa Nijeriya don kare Kiristoci,” yana mai cewa idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma “mai yiwuwa ta shiga ƙasar don kawar da ‘yan ta’adda masu zafin kishin Musulunci.”

Barazanar Trump ta jawo cece-kuce bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya, ba tare da ya bayyana takamaiman inda ya samo waɗannan alƙaluman ba.

Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Tinubu ya jaddada cewa Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai kiyaye dimokuraɗiyya, wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m