Aminiya:
2025-04-30@23:37:05 GMT

Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani

Published: 25th, March 2025 GMT

Samira Sani ‘yar asalin garin Kano ne da ta shigo Masana’anrtar Kannywood a 2022.

A tattaunarta da Aminiya, ta ba da tarihinta da kuma yadda ta daɗe tana mu’amala da ‘yan Kannywood kafin ta fara fitowa a fim:

Za mu so ki gabatar da kanki?

Suna na Samira Sani, jaruma a Masanartar Fim ta Kannywood.

Mene ne tarihinki a takaice?

To ni ‘yar asalin garin Kano ne.

An haife ni a garin Dakatsalle da ke Karamar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano.

Na yi makarantun firamare da sakandare duk a Dakatsalle, bayan na gama sakandare sai aka yi min aure, daga baya Allah Ya kawo ni cikin birnin Kano.

Ke nan kin taɓa yin aure?

Eh na taɓa yin aure, kuma ina da ‘ya’ya uku.

Ta yaya kika samu kanki a Kannywood?

Ta sanadiyyar wata ƙawata, wacce take ‘yar fim ce, tana gayyata ta, muna zuwa wurin daukar fim, a hankali a hankali, ‘yan Kannywood suka san ni, ni ma na san mutane.

A wace shekara kika shiga Kannywood?

Na shiga ne a shekara 2022, shekaru uku ke nan, amma ban fara fitowa a fim ba sai a shekarar 2023.

Me ya ba ki sha’awa kika shiga Kannywood?

A da gaskiya ba na sha’awar Kannywood.

Saboda me?

Saboda yadda ake zagin ‘yan fim, ana cewa ‘yan iska ne, to sakamakon na shiga cikinsu, na ga irin yadda suke da mu’amala mai kyau, suna son junansu, domin idan na je ana daukar fim, za ka ga ana wasa da dariya, har sai ka ji ba ka son rabuwa da su.

To a haka sai na fuskanci abin da ake faɗa a kan ‘yan fim ba gaskiya ba ne, wasu ne suke masa kallo a baibai.

To daga nan sai na ji ina sha’awar abin, to sai na fahimtar da iyayena da ‘yan’uwana, To a haka na shiga Kannywood, inda na fara a hannun Darakta Mujahid M. Soja.

To ke nan sai da kika fara mu’amala da ‘yan Kannywood sannan kika fara fim da su haka ne?

Kwarai kuwa, sai da na fara mu’amala da su sannan na shiga Kannywood, saboda a gaskiya a da ina dari-dari da shiga fim, ina gudun kar a ce mini ‘yar iska to amma da na yi mu’amala da su, sai na fahimce su, kuma na ga abin da ake yi a waje ba a yin sa a fim.

Domin ina mu’amala da ‘yan fim ina yi da wadanda ba ‘yan fim ba, shekara biyu ina mu’amala da ‘yan fim sannan na fara.

To da wane fim kika fara?

Na fara da wata waƙa ce mai suna Ladidi mai Koko da Sosai, wacce muka yi da dan Yarbawa da Kamal Aboki (marigayi) da Adam Dorayi.

A ɓangaren fim kuwa na fara da fim din ‘Yar Tiktok na Darakta Mujahid M. Soja.

Ya zuwa yanzu finafinai nawa ne kika yi?

Za su kai 8 zuwa 9, wadanda suka haɗa da: ‘Yan Tiktok da Soyayya Daya da Buri da Niniya da Umarni da kuma Jikokin Mai gari da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kannywood Samira Sani shiga Kannywood a Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

 Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma

Manyan malaman addinin darikar Roman Katolika za su fara Shirin zabar shugaban darikar tasu a fadar Vatican

Adadin manyan malaman addinin masu mukamin “Cardinal” 130 ne za su taru a fadar Vatican, domin su zabi wanda zai maye gurbin Paparoma Farancis da ya rasu.

Sai dai masu kusancin da fadar ta Vatican suna bayyana cewa, da akwai batutuwa da dama da su ka raba kawunan manyan malaman addinin na Roman Katolika da  su ka batun auren jinsi, da rawar da mata za su taka a karkashin inuwar cocin.

Sai dai kuma wani mai sharhi akan abubuwan da su ka shafi cocin, Reese ya bayyana cewa, masu zaben za su mayar da hankali ne akan wanda zai kare ayyukan da mamacin Paparoma Francis ya bari.

Tare da cewa babu kafa ta yin yakin neman zabe a tsakanin masu mukamin na Cardinal, sai dai da akwai wasu siffofi da halaye da ake son gani da wadanda za su iya zama ‘yan takara.

Ana sanar da wanda ya zama sabon Paparoma ne ta hanyar samun kaso 2/3 na kuri’un da manyan masu zaben su ka kada.

A bisa ka’idar cocin, duk wanda aka yi wa wankan tsarki na  ” Baptisma”zai iya zama paparoma,amma  kuma tun daga 1378 ba a zabi wanda bai kai mukamin “Cardinal” ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano