Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038
Published: 5th, August 2025 GMT
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raba wa sabbin ma’aikatan aikin gona 1,038 da aka dauka aiki takardun su na kama aiki.
Bikin, ya gudana ne a gidan gwamnatin Kano.
Da yake jawabi yayin bikin gwamnan ya gargade su da su guji cin hanci da rashawa, ya kuma bukace su da su yi wa jihar hidima cikin himma da gaskiya.
Ya ce matakin ya nuna wani gagarumin ci gaba a kokarin da jihar ke yi na inganta samar da abinci da kuma habaka arzikin iyali.
Gwamna Yusuf ya bayyana daukar ma’aikata a matsayin cika alkawuran da ya dauka a lokacin yakin neman zabe da kuma wani muhimmin mataki na cimma wadannan manufofin.
“Yau rana ce ta sabuwar dama da cika alkawarin da muka dauka a yakin neman zabe, wadannan ayyuka ba wai kawai za su tallafa wajen samar da abinci ba, har ma da samar da kudaden shiga ga dubban iyalan Kano.”
Gwamnan ya bayyana cewa, duk da cewa Kano ta riga ta jagoranci kasar nan wajen yawan ma’aikata, amma duk da haka jihar na bukatar karin biyan bukatun noma na zamani.
“Muna bukatar karin kwararrun ma’aikatan da za su yi wa al’ummominsu hidima, da tallafa wa manomanmu, da kuma taimakawa wajen kawo sauyi a fannin noma.”
Gwamna Yusuf ya gargadi sabbin ma’aikatan da su guji cin hanci da rashawa, rashin zuwa aiki, da rashin tausayi, yana mai jaddada cewa daukar ma’aikata ba wata hanya ce ta wawure dukiyar al’umma ba.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Borrell: Rashin tabuka komai daga Turai ya karfafa gwiwar Isr’ila wajen aikata laifuka
Tsohon jami’in harkokin wajen Tarayyar Turai Joesp Borrell, ya yi gargadi game da ci gaba da rashin taka rawar gani daga bangaren kasashen Turai dangane da ayyukan cin zarafin da Isra’ila ke ci gaba da yi, yana mai cewa irin wannan rashin hankali ya sa kungiyar Tarayyar Turai (EU) ta zama abokiyar tarayya a cikin laifukan da Isra’ila ke aikatawa.
Joesp Borrell ya bayyana hakan ne a cikin wani fashin baki wanda aka buga a cikin jaridar The Guardian ta kasar Burtaniya.
“Wadanda ba su yi aiki ba don dakatar da wannan kisan kiyashi da kuma keta dokokin kasa da kasa, duk da cewa suna da ikon yin wani abu kan hakan, to tabbas suna da hannu a cikin wadannan laifuka,” in ji shi.
Borrell ya ba da misali da yakin kisan kiyashi da gwamnatin kasar Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta kaddamar tun daga watan Oktoban 2023 a kan zirin Gaza wanda ya zuwa yanzu ya lakume rayukan Falasdinawa akalla 60,332, galibi mata da kananan yara, a matsayin babban misali.
Tsohon jami’in ya kuma yi tsokaci game da harin da ake kaiwa a matsugunan Falastinawa wa a kullum a yammacin gabar kogin Jordan.
EU, ta sha tabbatar da cewa ita ce babbar abokiyar kasuwanci ta gwamnatin Isra’ila, kuma babban mai saka hannun jari, kuma babban mai samar da makamai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa August 5, 2025 Baghaei : Ziyarar Pezeshkian a Pakistan ta bude wani sabon Shafin alaka August 5, 2025 Afirka ta Kudu ta zayyana matakan tallafi ga ‘yan kasuwa na cikin gida a matsayin martani ga harajin Trump August 5, 2025 Hamas ta musanta kalaman Witkoff game da batun mika makamanta August 5, 2025 Araqchi: Namijin kokarin al’ummar Iran abin yabawa ne August 4, 2025 Khatibzadeh: Iran ba za ta amince da saryar da hakkokinta ba a duk wata tattaunawa da Amurka August 4, 2025 Rahotonni: Agajin Jin kai Da Ake Jefawa Ta Sama A Gaza Ba Shi Da Tasiri August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci