Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
Published: 14th, April 2025 GMT
’Yan sanda sun kama shahararren mawaƙin zamani a Najeriya Habeeb Okikiola Badmus, wanda aka fi sani da Portable, bayan ƙazancewar rikicinsa da fitaccen ƙwararren mawakin Fuji, Okunola Saheed “Osupa.”
A ranar Lahadi da dare ne ’yan sanda daga Jihar Kwara suka yi takakkiya suka kamo Portable mai waƙar “Zazu Zeh” a garin Abeokuta, Jihar Ogun
Kakakin ’yan sanda na Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ya ce an kama Portable bayan samun takardar ƙorafin da Osupa ya aike ɗauke da jerin manyan zarge-zarge da yake yi wa mawakin na “Zazu Zeh,” na ɓata suna, barazanar kisa, tunzura jama’a, zubar da da mutum da gangan, neman tayar da fitina, da kuma amfani da zagi da munanan kalamai.
“Saboda girman waɗannan zarge-zarge da kuma ingantattun shaidun da aka gabatar, rundunar ta samu sammacin kame daga Kotun Majiatare da ke zamanta a Ilorin, inda jami’anmu suka je Abeokuta, suka kamo wanda ake zargin suka kawo shi Ilorin domin ci gaba da bincike.”
Jami’in ya ce da kawo Portable jihar Kwara, nan take aka fara yi masa Portable tambayoyi da ɗaukar bayanansa a gaban lauyoyi daga bangarorin biyu.
Ya tabbatar da cewa Portable zai ci gaba da kasancewa a tsare kuma nan ba da komawa ba za a gurfanar da shi a gaban kotu.
Rigimar mai zafi, tsakanin Portable da Osupa, ta samo asali ne daga rashin jituwa kan keta haƙƙin mallakar waƙa. Wannan rashin jituwa ta ɓarke ne a bainar jama’a lokacin da Portable ya yi amfani da zagi ga fitaccen mawakin na Fuji mai shekaru 55 a wani bidiyo da ya yaɗu, wanda ya jawo caccaka a kafafen sada zumunta.
A cikin bidiyo, Portable ya bayyana cewa, “Kuɗi ne ya jawo faɗan!” yana ƙoƙarin bayyana ɓacin ransa. Ya ce “Raina ya ɓaci ne saboda ina so a ba ni kuɗina, kuma na ji suna ƙoƙarin sauke waƙar.”
Bayan shan caccaka daga bisani ya saki wani bidiyo yana neman afuwar Osupa cikin girmamawa. Ya ce, “Sarki Saheed Osupa, babana, don Allah kada ka yi fushi. Ka ɗauke ni kamar ɗanka ka horar da ni.”
A wani yanayi mai ban mamaki kuma, Portable ya nuna cewa rigimar tasu wani salon neman magoya baya ne, har ma ya nemi a ba shi damar gudanar da wasanni. “Dukkanmu muna tallata kanmu… don Allah a ba ni aiki.”
Sai dai, Saheed Osupa ya yi watsi da neman afuwar a matsayin wanda bai isa ba, yana mai cewa dole Portable ya samu sakamakon abin da ya aikata.
Ƙi amincewar tasa ba ta yi wa Portable daɗi ba, har ya ƙi janyewa, inda a ƙarshe ya kai ga matakin da Osupa ya ɗauka na shigar da ƙara ga hukumar ’yan sanda.
Yanzu, duniyar nishaɗi ta zura ido tana kallon yadda za a ƙare a wannan rikici manyan mawaka da ya tashi daga kafafen sada zumunta zuwa zauren kotu.
Shin Portable zai fuskanci cikakken hukuncin doka bisa ga zarge-zargen da ake yi masa, ko kuwa za a samu sasanci ne?
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: mawaki Mawaƙi Portable ya
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
Aƙalla mutum 26 ne suka rasu sakamakon wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka a Jihar Binuwai.
Hare-haren sun faru ne a yankunan Ƙaramar Hukumar Makurdi da Katsina-Ala tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na daren ranar Alhamis.
Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasuA Ƙaramar Hukumar Makurdi, wasu ’yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Mtswenem da Akondotyough Bawa, inda suka kashe mutum 25.
Haka kuma, an kashe mutum ɗaya a wani hari daban da aka kai ƙauyukan Kenvanger da Agbami a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala.
Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun shiga gidajen mutane suna harbin su yayin da suke barci, suna amfani da bindigogi da adduna.
Wani wanda ya tsira mai suna Iorpuu, ya ce mata da yara suna cikin waɗanda aka kashe, kuma har yanzu ana neman wasu da suka ɓace.
Ya ƙara da cewa wasu sun mutu ne a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.
Wani ganau ya ce an fara kai harin ne wani ƙauye kusa da Jami’ar Noma da Fasaha ta Makurdi, inda aka kashe mutane huɗu.
Daga nan suka wuce wani ƙauye a kusa da unguwar Low Cost suka ci gaba da kashe mutane har adadin gawarwakin ya kai 25.
A Katsina-Ala, ’yan bindigar sun kai hari ƙauyukan Kenvanger da Agbami da misalin ƙarfe 1 na dare.
An ce sun yi yunƙurin yi wa wasu matan da suka haihu fyaɗe, amma mazan ƙauyen suka kai musu ɗauki.
Wannan ya haifar da rikici inda ’yan bindigar suka buɗe wuta, suka kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu.
A ƙauyen Agbami kuma, sun yi wa mutane da yawa dukan kawo wuƙa amma babu wanda ya mutu.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ya tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru a Makurdi.
Ya ce za su ci gaba da bai wa ’yan jarida bayanai, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani.