Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
Published: 25th, March 2025 GMT
Tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya ce mulkin dimokuraɗiyya ya gaza wajen kawo ci gaba a nahiyar Afirka.
Ya ce tsarin ya gaza ne saboda abin da ya ƙunsa bai zo daidai da al’adu, da yadda ake tafiyar da rayuwa a nahiyar ba, da abubuwan da mutanen nahiyar suka yi amanna da su ba.
Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren GwamnatiTsohon shugaban na wannan furuci ne a Abuja a wurin wani taron bikin cika shekaru 60 a duniya na tsohon mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai kuma tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha.
Obasanjo ya buga misali da yadda tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln, ya bayyana tsarin dimokuraɗiyya da cewa gwamnati ce ta mutane da mutane ke jagoranta domin al’umma.
Ya ƙara da cewa tsari ne da ake yu domin kowa ya amfana, ba wai wani ɓangaren na al’umma ba ko wasu mutane ƙalilan ba.
Obasanjo ya kuma bayyana cewa kafin zuwan dimokuraɗiyyar ƙasashen yamma, Afirka na da nata tsarin shugabancin wanda ke kula da buƙatun kowa.
A cewarsa wannan tsarin shi ne dimokuraɗiyya, ba abin da ake kira dimokuraɗiyya ba a yau wanda ke bai wa shugabanni damar karɓar duk abin da suke so ba bisa ƙa’ida ba da kuma ta hanyar cin hanci da rashawa su ce wa mutane su je kotu idan suna da ja.
Obasanjo ya ce matuƙar ba a sake fasalin dimokuraɗiyya ta yi daidai da al’adu da manufofin ’yan Afirka da kuma mutunta buƙatun jama’a ba, to za ta ci gaba da durƙushewa kuma a ƙarshe ta mutu murus a nahiyar.
Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar da tsoffin gwamnonin Anambra da Ribas —Peter Obi da Rotimi Amaechi.
Sauran mahalartan sun haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, tsoffin Shugabannin Majalisar Dattawa — David Mark da Ken Nnamani da tsoffin gwamnonin Sakkwato da Kuros Riba — Aminu Waziri Tambuwal da Donald Duke.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dimokuraɗiyya Obasanjo ya
এছাড়াও পড়ুন:
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Binciken likitoci da ‘yansanda ya tabbatar cewa gubar ce ta yi sanadin mutuwarsa.
Haka kuma, kotun ta yanke wa wani mutum mai suna Sani Sa’adu hukuncin ɗaurin shekara biyar saboda ɓoye gaskiya da ya yi dangane da wata Gift Bako, wadda ake zargi da hannu a kisan.
Lauyoyin waɗanda aka yanke wa hukunci sun nemi sassauci saboda suna da iyalai, amma lauyan gwamnati ya bayyana jin daɗinsa da hukuncin, inda ya ce an yi adalci kamar yadda doka ta tanada.
Rabe Nasir, ya taɓa zama ɗan majalisar tarayya da kuma kwamishinan Jihar Katsina a lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar Aminu Bello Masari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp