Leadership News Hausa:
2025-08-04@12:57:54 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

Published: 4th, August 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

Akalla mutane 11 ne aka kashe a harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a unguwannin Kagara da San-Isa da ke karamar hukumar Kaura-Namoda a jihar Zamfara. Majiyoyi daga yankunan biyu sun shaida wa wakilinmu cewa an kai hare-haren ne a unguwannin Kagara da San-Isa tare da wasu kauyukan da ke kewaye. Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu? Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi Wata majiya daga dan garin Kagara wanda ya bayyana sunansa da Abubakar Sani ya shaidawa LEADERSHIP cewa ya rasa ‘yan uwansa guda biyu a harin wanda ya afku a ranar Asabar din da ta gabata.

Ya ce, ‘yan fashin da suka yiwa kauyen su kawanya da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Asabar, sun yi awon gaba da shanu da sauran kayayyakin mutane tare da yin garkuwa da maza da mata zuwa cikin daji. Da yake zantawa da LEADERSHIP ta wayar tarho, wani mazaunin garin, Ahmed Dan-Isa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kashe akalla mutanen kauyen 9 a ranakun Asabar da Lahadi da safe tare da yin garkuwa da wasu da dama da suka hada da maza da mata. Ahmed wanda ya ce ya tsere daga hare-haren ‘yan bindigar, amma ya ce, maharan sun mamaye kauyukan ba tare da fargabar jami’an tsaro ba. Ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta tarayya da su taimaka ta hanyar kubutar da daukacin Kaura-Namoda daga mummunan halin da take ciki. Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda (PPRO) na rundunar, Yazid Abubakar ya ci tura, domin lambar wayarsa a kashe take a lokacin hada wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Bugu da ƙari, Hukumar ta NPA ta bayyana cewa, tana kan ƙoƙarin inganta kayan aiki Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar, wanda ta zuba dala biliyan daya, domin fara gyaran Tashoshin Jiragen Ruwa ta Tin Can Island tare da yin ayyukan kwakwarima, a Tashoshin Jiragen Ruwa na, Apapa, Riɓers, Onne, Warri da kuma Kalaba.

Ita kuwa a na ta ɓangaren, Kwalejin ta MAN ta bayyana cewa, nauyin da aka ɗora mata na gudanar da ayyukan ta, son yi daidai da ƙoƙarin ƙasar nan ke ci gaba da yi, na ƙara haɓaka tattalin arzikin ƙasar, mussaman wajen yaye haziƙai kuma ƙwararrun ɗirebobin Jiragen Ruwa da ƙasar nan ke buƙata.

Shugaban Hukumar ta NPA darka Abubakar dantsho, a jawabinsa ewabinsa a taron shekara- shekara na ƙasa na shekarar 2025 na  ƙungiyar ƴanjarida da ke dauko rahotabin da suka shafi fannin ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa wato AMJON ta gudanar a dakin taro na otel ɗin Sheraton Hotel da ke a, Ikeja a jihar LegasLegas, ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA,  na kan gudanar da aikin fadada Sabbin Tashoshin Jiragen Ruwa na Snake Island, Badagry ɗeep Seaport, Ondo ɗeep Seaport da kuma ta,  Burutu wadanda daukacin aikin, a yanzu suka kai matakin kammalawakammalawa

dantsho wanda  Babbar Manajar  huɗda da Juma’a a Hukumar ta NPA Hadiza Usman Shu’aibu ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA, ta mayar da hankali wajen ganin tana ƙara daga nartabar kayan aikinta da ke a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwa na ƙasar,mussaman ta hanyar sanya masu kayan aiki na zamani, domin a rinƙa Kula da saukar Jiragen Ruwa da ƙara janyo masu zuba hannun jari, a fannin.

Shugaban ya ci gaba da cewa, a yanzu haka, Nijeriya ta samu samar shiga cikin ƙungiyar ƙasa da ƙasa ta Kula da tsara Tashoshin Jiragen Ruwa wato IPCSA wanda ya samar da cewa, wannan shigar ta Nijeriya cikin ƙungiyar, zai bai wa Nijeriya damar wanzar da tsarin NSW wanda aka samar da shi, bisa nufin saita ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da kuma rage ƙalubalen da ake fuskanta ta hada-hadar kasuwanci.

Kazalika, dantsho ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA, ta samu nasarar rage ƙalubalen cunkodon ababen hawa da ake fuskanta a  Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
  • Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa 1 Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci
  • ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa