An sace jaririya sabuwar haihuwa a asibitin Ekiti
Published: 4th, August 2025 GMT
An nemi wata jaririya saoi kaɗan bayan haihuwarta an rasa a Cibiyar Lafiya ta Okeyinmi da ke Ado-Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, a ranar Litinin.
Wani ganau ya ce an gano ɓatan jaririyar ne lokacin da ma’aikatan jinyar da ke bakin aiki suka je su duba lafiyarta da safiyar wannan Litinin ɗin.
Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙuraLamarin na ba-zato-ba-tsammani ya haifar da fargaba musamman yadda ɗimauta uwar jaririyar da kuma wasu daga cikin mutanen da ke cikin harabar asibitin.
Tuni dai an garzaya da ma’aikatan da ke kula da ɗakin haihuwa da uwar jaririyar da mai gadi da wasu da ake zargi zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.
Aminiya ta ruwaito cewa wasu masu neman na abinci a kusa da asibitin sun shiga ɗimuwa matuƙa dangane da faruwar lamarin.
Mai magana da yawun rundunar ’yan sanda na jihar, SP Sunday Abutu, ya ce yanzu haka akwai mutum huɗu da ake zargi da suka shiga hannu, “kuma suna bayar da bayanai masu amfani da za su taimaka a binciken.”
Abutu ya ce Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Mista Joseph Eribo, ya umurci sashen bincike na musamman (CID) da su gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da dawo da jaririyar cikin ƙoshin lafiya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
Bankin Raya Ci-gaban Afirka (AfDB) ya amince da ba wa Gwamnatin Jihar Sakkwato bashin Naira biliyan 70.4 domin inganta fannin kiwon lafiya.
Wannan shiri na da nufin bunƙasa fannin kiwon lafiya da ingancinsa, da kuma cike giɓin da ake da shi a ɓangaren a Jihar Sakkwato, a cewar AfDB ta bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a.
Rahotanni na nuni da cewa, yaro ɗaya cikin kowane yara 20 ne akale yi wa allurar rigakafi cikakke a Jihar Sakkwato a, a yayin da adadin mutuwar jarirai ya kai 104 daga cikin 1,000 a Jihar.
Ƙasa da kashi 14 cikin 100 na cibiyoyin lafiya a jihar ne suke da kayan aiki masu aiki, kuma likita ɗaya ne kawai ke kula da mutum 8,285, wanda ya gaza abin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayar na likita 1 ga 1,000 mutum.
Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPPKuɗaɗen da bankin ya ware za su tallafa wa samar kayan aikin kula da lafiya masu inganci a matakai uku na kula da lafiya a Jihar Sakkwato.
Wannan ya haɗa da gina sabon asibitin koyarwa mai gado 1,000, da manyan asibitoci na yankuna uku masu jimillar gadaje 450, da kuma cibiyoyin kiwon lafiya guda shida da aka tsara a domin kuka da al’ummomin karkara.
Aikin ya kuma haɗa da gyaran cibiyoyin horar da ma’aikatan lafiya da ƙirƙirar sabon ma’ajiyar magunguna ta zamani.
Darakta-Janar na Ofishin AfDB a Najeriya, Abdul Kamara, ya ce, “Wannan rancen na nuna yadda muke jajircewa wajen aiki tare da gwamnati don magance giɓin kayan kiwon lafiya a Najeriya, tare da gina cibiyoyin kula da lafiya masu ƙarfi da suka dace da tsari na yanayi.
“Ta hanyar ƙarfafa kayan aikin lafiya a Jihar Sakkwato, muna gina fata da hanyoyin samun kyakkyawan sakamako ga miliyoyin ’yan Najeriya.”