Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
Published: 14th, April 2025 GMT
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran babban titin Abuja-Kaduna-Zariya-Kano, wadda ke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Arewacin Najeriya.
Da yake jawabi a taron kaddamarwar a Kagarko, Jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani, ya bayyana yadda aka yi watsi da hanyar da kuma irin mummunan tasirin da hakan ya yi ga rayuka da ci-gaban tattalin arziki.
Gwamna Uba Sani, ya yaba wa Tinubu bisa farfado da aikin, yana mai nuni da muhimmancin hanyar a matsayinta na mafi yawan zirga-zirgar ababen hawa a Arewa.
Da yake ba da tabbacin kamma aikin a cikin watanni 14, Tinubu wanda Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce za a gina titin ne da kankare, kamar babbar hanyar Legas zuwa Kalaba.
An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken TinubuMinistan ya kara da cewa aikin zan dangana har zuwa filin jirgin sama na Kano, kuma za a sanya kyamarorin CCTV gaba daya a tsawon titin, wanda sabon dan kwangila ne zai aiwatar.
Ya ce, shugaban kasa ya amince da naira biliyan 252 don muhimman sassan aikin, inda aka riga aka biya kashi 30%, yanan mai yaba muhimmiyar rawar da Gwamna Uba Sani ya taka a aikin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: aikin gyara
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da tsaro a duk lokacin bukukuwan Easter.
Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar jihar, ASCII Umar Mohammad M. ya fitar, ya ce jami’an sun jibge a wuraren ibada daban-daban da sauran muhimman wurare a fadin kananan hukumomi 14 na jihar domin tabbatar da tsaro da kuma gudanar da bukukuwan lafiya.
A cewar sanarwar, kwamandan jihar, Sani Mustapha, ya jaddada kudirin hukumar NSCDC karkashin jagorancin kwamandan Janar, Dakta Ahmed Abubakar Audi, na magance matsalolin tsaro a fadin kasar nan.
Ya kuma tabbatar da cewa rundunar a jihar Zamfara ta shirya tsaf domin gudanar da ayyukanta yadda ya kamata tare da bayar da gudumawa wajen wanzar da zaman lafiya a jihar.
REL/AMINU DALHATU