Gwamnatin tarayya ta ce tace a shirin ta sauya wuraren dake bushe a sassan arewacin Nijeriyaza a raba naira miliyan  miliyan 3.4 kuma akasarin wadanda zasu amfana da wannan za su kasance mata ta hanyar Shirin ACReSAL.

 

Da yake jawabi a wajen bude taron kwanaki 10 na masu ruwa da tsaki kan tsarin kula da tsare-tsare (SCMP) na sabbin magudanan ruwa guda 11 a fadin Jihohi bakwai na tarayya a Ilorin, kodinetan ayyukan ACRESAL na kasa, Mista Abdulhamid Umar, ya ce za a gudanar da aikin ne ta hanyar shirin kawo sauyi na dogon lokaci.

 

Jami’in kula da ayyukan na kasa na ACRESAL Adamu Shettima wanda ya samu wakilcin kwararre a bangaren kula da ayyukan ruwa na gwamnatin tarayya, Adamu Shettima, ya bayyana cewa aikin yana da nasaba da dawo da martabar yankuna da suke bushe, daidaita yanayin muhalli da kuma karfafa miliyoyin al’umma a fadin Arewacin Najeriya.

 

Umar ya bayyana cewa bankin duniya ne ke taimaka wa aikin ta hannun kungiyar ci gaban kasa da kasa (IDA), ya kara da cewa wannan shi ne karon farko da gwamnatin tarayya ke samar da tsarin kula da ruwa mai girman irin wannan.

 

Ya yi nuni da cewa, dabarun da masu ruwa da tsaki za su mayar da hankali wajen yin mu’amala da masu ruwa da tsaki a dabarun da suka shafi Kwara, mai masaukin baki, Kaduna, Kebbi, Zamfara, Niger da FCT.

 

A nata jawabin, kwamishiniyar muhalli ta jihar Kwara, Hajia Nafisat Musa Buge, ta bayyana cewa hadakar masu ruwa da tsaki na daga cikin shirin inganta sha’anin ruwa, da inganta yanayin da ake ciki, da inganta rayuwa mai ɗorewa a yankunan da ke fama da wannan matsala a Najeriya.

 

Kwamishinan, ta ce sabon Shirin zai kasance ne tsakanin jihohi shida na Najeriya.

 

A nasa jawabin, Ko’odinetan shirin ACRESAL na jihar Kwara, Alhaji Shamsideen Aregbe, ya bukaci a hada kai da masu ruwa da tsaki wajen samar da tsare-tsare na kula da ruwan.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara masu ruwa da tsaki

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa

Hukumar Yaki da Hamada da Sauyin Yanayi ta Kasa ta kammala shirye-shiryen dasa itatuwan dabino miliyan hamsin (50,000,000) a jihohi goma sha ɗaya 11 da ke fama da fari a Najeriya.

Daraktan Hukumar, Alhaji Salihu Abubakar ne ya bayyana hakan a lokacin ƙaddamar da shirin dasa itatuwan dabinon da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

Ya ce za a dasa itatuwan dabino guda dubu dari biyar (500,000), tare da wasu nau’o’in itatuwa na gida a faɗin jihar Jigawa.

Alhaji Salihu Abubakar ya yi kira ga jama’a da su rungumi al’adar dasawa da kula da itatuwa domin magance matsalolin hamada, zaizauar ƙasa da sauyin yanayi.

A cewarsa, Hukumar tana aiki tukuru a jihohin da ke  fama da fari a Najeriya don yaƙi da hamada, farfaɗo da wuraren da suka lalace a sanadiyar girgizar kasa,, da kuma inganta rayuwar al’ummar karkara.

Ya ce bisa  shirin dasa itatuwa, da kuma amfani da albarkatun ƙasa ta hanyar haɗin gwiwar al’umma, Hukumar ta dasa miliyoyin itatuwa tare da farfaɗo da wuraren da ke tallafa wa rayuwa a yankunan da fari ke addaba.

Daga ƙarshe, ya nuna jin daɗinsa bisa jajircewar da gwamnatin jihar Jigawa ta nuna wajen karɓar bakuncin wannan biki na shekara-shekara da aka gudanar a Dutse.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa
  • Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci  Sun Bayyana Cewa: Masu Shirin Halaka Gaza Suna Son Mamaye Duniyar Musulmi Ne
  • Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
  • Shirin ACRESAL Zai Samar Da Injinan Ban Ruwa Masu Amfani Da Hasken Rana A Jigawa
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji