Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-25@03:01:11 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma

Published: 14th, April 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma

Gwamnatin Jihar Jigawa ta siyo tan tan guda 360 domin tallafawa manoma don ci gaba da habbaka harkokin noma a Jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin kaddamar da shirin noman rani na shinkafa a kauyen Jura dake Karamar Hukumar Auyo.

Ya yi bayanin cewar, gwamnatin ta kuma siyo injin girbin shinkafa guda 70 da sauran kayayyakin noma domin tallafawa manoman shinkafa.

A don haka, Gwamna Umar Namadi ya yi gargadin hukunta duk wanda aka samu ya karkatar da kayayyakin aikin gona da gwamnatin ta samarwa manoman jihar.

Yana mai cewar, fiye da manoma dubu hamsin da biyar ne za su amfana da shirin, wanda wani bangare ne na kokarin gwamnati na bunkasa aikin gona da wadata kasa da abinci.

Kazalika, Gwamnan ya kaddamar da rabon Babura 300 ga malaman gona domin wayar da kan manoma.

Ya kuma bayyana irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu wajen bunkasa harkokin noma.

A cewar sa, wannan shirin yana daya daga cikin muhimman manufofi 12 da gwamnatinsa ta sanya a gaba, wadanda suke daidai da manufofin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na samar da wadataccen abinci ga ‘yan Najeriya.

Namadi ya bayyana cewar, tallafawa harkar noma da samar da malamai a fannin gona na daga cikin manyan hanyoyin cimma burin gwamnati na wadatar abinci da habaka tattalin arziki.

Ya kuma yaba da hadin kai da goyon bayan da manoma ke bayarwa wajen aiwatar da irin wadannan shirye-shiryen da gwamnati ke bullowa da su.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kananan manoma za su samu rangwamen kashi 30 cikin 100, yayin matsakaita za su amfana da kashi 20, manyan manoma kuma za su samu kashi 10 akan kayayyakin da za su siya.

Kayayyakin da aka raba sun hada da injinan ban ruwa da takin zamani da magungunan kashe kwari da sauran su.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa

Hukumar Raya Kogunan Hadejia da Jama’are (H-JRBDA) ta yi alƙawarin ɗaukar matakan gaggawa don magance matsalar ambaliyar ruwan da ke addabar al’ummar Ƙaramar Hukumar Jahun a Jihar Jigawa.

Manajan Daraktan Hukumar, Injiniya Rabi’u Sulaiman Bichi, ya bayyana hakan bayan karɓar roƙon da jama’ar yankin suka miƙa ta hannun Shugaban Ƙaramar Hukumar, Jamilu Ɗan Malam Mai Rice, kan yawaitar ambaliya a yankin.

Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya

A cewar Injiniya Bichi, “Mun karɓi kokenku hannu biyu. Matakin da shugabancin Jahun ya ɗauka ya yi dai-dai. Za mu tura ƙwararrun injiniyoyi su yi aikin da ya kamata domin daƙile ambaliyar, tare da inganta noman yankin ta hanyar gina madatsar ruwa domin ruwan sha da na aikin gona.”

A nasa bangaren, Shugaban Ƙaramar Hukumar Jahun, Hon. Jamilu Ɗan Malam Mai Rice, ya ce sun gabatar da koken ne saboda matsalar ambaliyar ta daɗe tana addabar su ba tare da samun mafita ba.

Ya ce, “Muna godiya bisa yadda kuka amsa kiranmu. Kun zo kun duba matattarar ruwan Akama da ta Fande tare da ƙwararrun injiniyoyinku. Wannan ya nuna ku na da niyyar magance matsalar da ta dade tana damunmu.”

Tawagar hukumar da ta kai ziyarar ta haɗa da Daraktan Kuɗi da Mulki, Musa Iliyasu Kwankwaso; Daraktan Tsare-tsare, Alhaji Tijjani Musa Isah; Daraktan Na’urori, Injiniya Dan Baffa Abdulƙadir; da Injiniya Sabi’u Ɗan Malan, tare da sauran manyan jami’an hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar
  • H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Mayar Da Rarar Kudi Ga Maniyyatan 2026
  • Tuƙin ganganci: KASTELEA  Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
  •  Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno