Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-14@19:57:42 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma

Published: 14th, April 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma

Gwamnatin Jihar Jigawa ta siyo tan tan guda 360 domin tallafawa manoma don ci gaba da habbaka harkokin noma a Jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin kaddamar da shirin noman rani na shinkafa a kauyen Jura dake Karamar Hukumar Auyo.

Ya yi bayanin cewar, gwamnatin ta kuma siyo injin girbin shinkafa guda 70 da sauran kayayyakin noma domin tallafawa manoman shinkafa.

A don haka, Gwamna Umar Namadi ya yi gargadin hukunta duk wanda aka samu ya karkatar da kayayyakin aikin gona da gwamnatin ta samarwa manoman jihar.

Yana mai cewar, fiye da manoma dubu hamsin da biyar ne za su amfana da shirin, wanda wani bangare ne na kokarin gwamnati na bunkasa aikin gona da wadata kasa da abinci.

Kazalika, Gwamnan ya kaddamar da rabon Babura 300 ga malaman gona domin wayar da kan manoma.

Ya kuma bayyana irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu wajen bunkasa harkokin noma.

A cewar sa, wannan shirin yana daya daga cikin muhimman manufofi 12 da gwamnatinsa ta sanya a gaba, wadanda suke daidai da manufofin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na samar da wadataccen abinci ga ‘yan Najeriya.

Namadi ya bayyana cewar, tallafawa harkar noma da samar da malamai a fannin gona na daga cikin manyan hanyoyin cimma burin gwamnati na wadatar abinci da habaka tattalin arziki.

Ya kuma yaba da hadin kai da goyon bayan da manoma ke bayarwa wajen aiwatar da irin wadannan shirye-shiryen da gwamnati ke bullowa da su.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kananan manoma za su samu rangwamen kashi 30 cikin 100, yayin matsakaita za su amfana da kashi 20, manyan manoma kuma za su samu kashi 10 akan kayayyakin da za su siya.

Kayayyakin da aka raba sun hada da injinan ban ruwa da takin zamani da magungunan kashe kwari da sauran su.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Na Ɗauki Harkar Fim Tamkar Aikin Gwamnati — Maryam Usman

An haife ni a garin Kano, amma asalina ‘yar Adamawa ce, kuma asalina ‘yar Maiduguri ce, sannan kuma yaren Margi ce ni. Bayan na girma a Kano na fara karatu a makarantar sojoji ‘Bokabo Barrack’, daga nan muka bar ‘Katsina Road’ muka koma ‘Yar Akuwa. Na fara firamare ‘Gidan Gona Special Primary School’. Bayan nan na tafi ‘Jigawa state’ wato Malam Madori, a ‘first time’ ‘yar’uwata ta rasu. Aka canja min makaranta aka dawo da ni ‘Gobernment Secondary School Kura’, a nan na kammala aji shida. Daga nan na tafi ‘Federal Polytechnic Yola’ a nan na karasa karatuna wanda nake da diploma. A yanzu kuma ina Na’ibawa a nan na girma, a nan aka yi min aure, yanzu komai nawa da Na’ibawa nake ‘bearing’.

 

Wane rawa ki ke takawa a cikin masana’antar Kannywood?

Ina taka rawa matsayin jaruma, kuma ina fitowa a matsayin mahaifiya me fadakarwa a cikin Kannywood, duk fim din da za a yi a uwa nake fitowa ba a taba canja min rol ba, kuma na san ba za a taba canja min rol din ba. Saboda ina aktin din iyaye, abin da iyaye suke yi shi nake yi. Shi ya sa a kowane fim za ki ga ana sha’awar saka ni na fito a uwa.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?

Ni dai na san abu ne me kyau, sannan kuma fadakarwa ne. Tun ina sakandare nake yin harkar fim. Babban abin da ya ja hankali na fadakarwar da fim yake, in kana son sako ya isa a minti daya to, harkar fim ita kadai za ta iya wannan abun,

 

Za ki yi kamar shekara nawa da fara fim?

Bayan na fito daga gidan mijina na dan kwan biyu ina wasu ‘business’ dina na harkar abinci, sai kuma na zo na shiga fim. Ban fi shekara biyu ba sai na yi aure, bayan na yi auren kuma da wasu shekaru sai na dada fitowa. Amma daga farawata zuwa yanzu zan yi shekara goma zuwa sha daya da harkar fim.

 

Ya gwagwarmayar shiga cikin masana’antar ta kasance?

Ni ban sha wata gwagwarmaya ba, saboda Sadik N-Mafia shi ya kai ni fim. Da akwai wata mawakiyar Sadi Sidi Sharifai wato Ummi Nagarta, ‘yar’uwa take a guna. Lokacin muna harkar siyasa an ba ni ‘women leader’ na ce mata ina son fim. Lokacin ina ta tunanin ina zan samu Sadik N-Mafia, ta ce to, tunda dan’uwanta ne na zo ta kai ni wajensa. Muna zuwa wajensa washegari na siyi ‘form’, wata washegarin aka fara fim da ni wani fim wai shi ‘Magana Jari’, aka ba ni wani rol me karfi, ban sha wahala ba. Da yake mu fim din kamar a jinin mu yake, ina da ‘yan’uwa da yawa a cikin Kannywood din nan, akwai; Halima Atete, Teemah Makamashi, Isma’il Fish, Aisha Humairan Rarara wacce ‘ya ce a guna uwarta aminiyata ce, sannan akwai Bana, sannan Stephening ta Arewa24 ‘yar’uwata ce to, kin ga mu mun mayar da fim sana’a.

 

Ya batun iyaye lokacin da za ki sanar musu kina sha’awar fara fim, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?

Gaskiya ban samu wata matsala ba, saboda akwai kanwata ana ce mata Sadiya ta rasu ita ta fara yin fim a gidanmu, har su Atete duk a bayanta suka yi fim. Sannan kuma mahaifiyata da mahaifina wayayyu ne duk abin da yaro yake so, indai ba na batanci bane suna so. Ko lokacin da na shiga fim mahaifina ya rasu sai mahaifiyata, zan iya lissafo miki manyan Kannywood wadanda suka san mahaifiyata wacce suka zo gabanta suka yi mata bayani ta ba ni ‘direct ticket’ ta ce na je, kuma a gabansu ta saka min albarka kuma har yau albarkar ce take dawainiya da ni.

 

A baya kin yi maganar kin fara fim me suna Magana Jari, ya karbuwar fim din ya kasance ga su masu kallon a lokacin?

Eh, na fara da Magana Jari, za ki ga ana yawan nuna shi a DSTB, sannan na zo na yi wani fim Sarka, lokacin ban waye ba sosai. Jamila Nagudu ce ta zaunar da ni ta ce in daina tsoron ‘Camera’, na tsaya na bude idona nayi abu me kyau, shi ma fim din ya karbu. Sannan na zo nayi Ibro Me Kilago, shi ma ya karbu sosai. Sannan a yanzu duk wani fim da ake yi a duniya indai aka saka ni za ki ga fim din ya fashe sosai, saboda wannan tijarar da nake yi.

 

Ya farkon farawar ya kasance?

Za ki ji na ce na tsoraci ‘camera’ Jamila ta gyara min, wannan shi ne na uku. Haske ne ya sa na tsoraci ‘Camera’, amma ko ranar da aka fara dora min ‘canera’ tambayata aka yi ta yi “daman kin saba yin fim?” na ce wannan ne na farko. Amma abin da ya sa ya yi kyau, wannan addu’ar mahaifiyar tawa ce. A fim dina na farko shi ne na hadu da Adaman Kamaye, ba na mantawa mun yi wasu finafinai muka fada tarkon ‘yan sanda ta dauko ni a motarta, muka dawo gida. Wannan shI ne dawowata na biyu kuma sai na dawo da daukaka da albarka.

 

Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?

Wai! ai finafinan da na yi sun fi dari, bana iya kirga su, saboda ni a wata zan iya yin fim ashirin.

 

Ko za ki iya lissafowa masu karatu kadan daga ciki?

Akwai; Lulu da Andalu na darakta Dan Hausa, Mashahuri na Yakubu Muhammad, Mage da Wuri na Hussaini Bacci, Manyan Mata na Abdul Amart, So Ne na Sultan, Garwashi na Uk, Lokaci na Tijjani Asase. To, suna da yawa gaskiya.

 

Cikin finafinan da ki ka fito, wane fim ne ya zamo bakandamiyyar ki?

Kowane fim bakandamiyata ce, ko ‘comedy’ na yi sai ya zama bakandamiyata.

 

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta tun daga farkon shigarki masana’antar, zuwa yanzu?

Kalubalen da na fuskanta wata mata ce wacce ta tsaya tana ta tsine min a kan an saka ni a fim din Garwashi, ta ce na takurawa ‘ya ta. Amma na ga tsohuwa ce bata fuskanci mene ne fim ba, shi kadai ne kalubale na. Kuma ban ji haushi ba, da yake sana’a ta ce, ita bata san mene ne fim ba.

 

Wadanne irin nasarori ki ka samu game da fim?

A cikin wannan masana’antar ta Kannywood na samu wata daukaka ta zama ‘Women leader’ a kungiyar Adon Garin Kasar Hausa, ta rantsar da ni a matsayin shugabar mata a Jihar Kano ranar litinin. Da na a makaranta ya samu babban mukami a dalilin uwarsa ‘yar fim ce, sannan ‘ya ta, ta sami babban mukami a dalilin uwarta ‘yar fim ce. Kuma lokacin da aka tura min ita garin iyamurai aka ce ta je bautar kasa, da na je a take babu abin da na kashe aka ba ni inda nake so wato Maiduguri garinmu. Sannan kuma na samu kyaututtuka da dama wanda ba sai na bayyana ba, to, kin ga ni ba zan iya barin fim ba. Na samu abubuwa da yawa kudade, kayan sakawa, alfarma a asibiti, ‘yan’uwana sun sassami alfarma da yawa a dalilina. Kuma ‘yan’uwana da yawa suna aikin gwamnati a dalilin harkar fim na sassamu alfarma da yawa.

 

Ya ki ka dauki fim a wajenki?

Na dauki fim babbar sana’a, saboda yadda dan gwamnati yake jin kansa a aikin gwamnati, haka nake jin kaina a aikin fim. Yadda dan majalisa yake jin kansa a ofis, haka nake jin kaina. Kuma yadda shugaban kasa yake jin kansa yana da mulki a karkashin ikonsa, haka nake jin dadi ina fim ina fadakar da mutane,

shi ne sana’a ta.

Za mu ci gaba a makon gobe

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Nishadi Tun Ina Yarinya Sana’ar Fim Ke Burge Ni —Hafsat Salisu November 30, 2025 Nishadi Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA November 15, 2025 Nishadi Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu November 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Akwai fargaba kan noman ranin bana
  • Na Ɗauki Harkar Fim Tamkar Aikin Gwamnati — Maryam Usman
  • An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa