Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-07@22:28:23 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma

Published: 14th, April 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma

Gwamnatin Jihar Jigawa ta siyo tan tan guda 360 domin tallafawa manoma don ci gaba da habbaka harkokin noma a Jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin kaddamar da shirin noman rani na shinkafa a kauyen Jura dake Karamar Hukumar Auyo.

Ya yi bayanin cewar, gwamnatin ta kuma siyo injin girbin shinkafa guda 70 da sauran kayayyakin noma domin tallafawa manoman shinkafa.

A don haka, Gwamna Umar Namadi ya yi gargadin hukunta duk wanda aka samu ya karkatar da kayayyakin aikin gona da gwamnatin ta samarwa manoman jihar.

Yana mai cewar, fiye da manoma dubu hamsin da biyar ne za su amfana da shirin, wanda wani bangare ne na kokarin gwamnati na bunkasa aikin gona da wadata kasa da abinci.

Kazalika, Gwamnan ya kaddamar da rabon Babura 300 ga malaman gona domin wayar da kan manoma.

Ya kuma bayyana irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu wajen bunkasa harkokin noma.

A cewar sa, wannan shirin yana daya daga cikin muhimman manufofi 12 da gwamnatinsa ta sanya a gaba, wadanda suke daidai da manufofin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na samar da wadataccen abinci ga ‘yan Najeriya.

Namadi ya bayyana cewar, tallafawa harkar noma da samar da malamai a fannin gona na daga cikin manyan hanyoyin cimma burin gwamnati na wadatar abinci da habaka tattalin arziki.

Ya kuma yaba da hadin kai da goyon bayan da manoma ke bayarwa wajen aiwatar da irin wadannan shirye-shiryen da gwamnati ke bullowa da su.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kananan manoma za su samu rangwamen kashi 30 cikin 100, yayin matsakaita za su amfana da kashi 20, manyan manoma kuma za su samu kashi 10 akan kayayyakin da za su siya.

Kayayyakin da aka raba sun hada da injinan ban ruwa da takin zamani da magungunan kashe kwari da sauran su.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), ta kammala fitar da jadawalin Rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026.

Za a gudanar da gasar ne a Amurka, Kanada da Mexico daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026.

Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara

Rabon jadawalin ya gudana ne a birnin Washington na ƙasar Amurka a ranar Juma’a, inda Ingila ta samu kanta a rukuni ɗaya Croatia.

Brazil za ta kara da Maroko, yayin da Amurka za ta kara da Australia.

Faransa za ta ɓarje gumi da Senegal, sannan Argentina za ta fafata da Austria.

Ga jerin yadda kowane rukuni na gasar Kofin Duniya na 2026 ya kasance:

Rukuni A: Mexico, Afirka ta Kudu, Koriya ta Kudu, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar.

Rukuni B: Kanada, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Qatar, Switzerland

Rukuni C: Brazil, Maroko, Haiti, Scotland

Rukuni D: Amurka, Paraguay, Australia, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar.

Rukuni E: Jamus, Curaçao, Ivory Coast, Ecuador.

Rukuni F: Netherlands, Japan, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Tunisia.

Rukuni G: Belgium, Masar, Iran, New Zealand.

Rukuni H: Spain, Cape Verde, Saudi Arabia, Uruguay

Rukuni I: Faransa, Senegal, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Norway

Rukuni J: Argentina, Aljeriya, Austria, Jordan.

Rukuni K: Portugal, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Uzbekistan, Colombia

Rukuni L: Ingila, Croatia, Ghana, Panama

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
  • Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki