Hukumar Yaki da Hamada da Sauyin Yanayi ta Kasa ta kammala shirye-shiryen dasa itatuwan dabino miliyan hamsin (50,000,000) a jihohi goma sha ɗaya 11 da ke fama da fari a Najeriya.

Daraktan Hukumar, Alhaji Salihu Abubakar ne ya bayyana hakan a lokacin ƙaddamar da shirin dasa itatuwan dabinon da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

Ya ce za a dasa itatuwan dabino guda dubu dari biyar (500,000), tare da wasu nau’o’in itatuwa na gida a faɗin jihar Jigawa.

Alhaji Salihu Abubakar ya yi kira ga jama’a da su rungumi al’adar dasawa da kula da itatuwa domin magance matsalolin hamada, zaizauar ƙasa da sauyin yanayi.

A cewarsa, Hukumar tana aiki tukuru a jihohin da ke  fama da fari a Najeriya don yaƙi da hamada, farfaɗo da wuraren da suka lalace a sanadiyar girgizar kasa,, da kuma inganta rayuwar al’ummar karkara.

Ya ce bisa  shirin dasa itatuwa, da kuma amfani da albarkatun ƙasa ta hanyar haɗin gwiwar al’umma, Hukumar ta dasa miliyoyin itatuwa tare da farfaɗo da wuraren da ke tallafa wa rayuwa a yankunan da fari ke addaba.

Daga ƙarshe, ya nuna jin daɗinsa bisa jajircewar da gwamnatin jihar Jigawa ta nuna wajen karɓar bakuncin wannan biki na shekara-shekara da aka gudanar a Dutse.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa dasa itatuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta

Hukumar bunkasa ilimin gaba da sakandare ta jihar Jigawa ta shirya taron tattaunawa ga jami’an gudanar da shirin koyawa dalibai musamman wadanda suke da nakasu a jarrabawar NECO ko WAEC wato Remedial program don su sami nasarar cin jarrabawar da za ta basu damar ci gaba da karatu a makarantun gaba da sakandare.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban hukumar, Dr Abbas A Abbas ya bayyana cewar gwamnatin jihar jigawa karkashin jagorancin Malam Umar Namadi ta sahalewa hukumar gudanar da shirin da ta saba yi duk shekara wajen baiwa daliban da suka fadi a jarrabawar NECO ko WAEC koyarwa ta musamman.

Yana mai cewar, sahalewar na da nufin basu damar sake rubuta jarrabawar don su sami dukkanin abun da ake bukata da zai basu damar ci gaba da karatun gaba da sakandare.

Dr Abbas A Abbas yace wannan shirn daya ne daga irin shirye shiye guda 6 da hukumar ke gudanarwa wanda doka ta basu dama.

Ya kuma kara da cewar, makasudin wannan tattaunawar shine a zaburar da jami’an kan irin aikin dake gaban su na ilimantar da dalibai hanyoyin da za su bi wajen amsa tambayoyin da akeyi a jarrabawar NECO ko WAEC.

Yace hakance tasa hukumar ta gayyato kwararrun masana don su kara bayar da bita ga jami’an a fannonin jarrabawar da ta shafi turanci da lissafi da kuma irin kalubalen da dalibai kan fuskanta wajen amsa tambayoyin alokacin jarrabawa.

Dr Abass ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi wajen kokarin sa na bunkasa harkar ilimi wanda daya ne daga cikin kudure kuduren sa 12 na ciyar da jihar gaba.

A jawaban su daban daban, kwararriya mai baiwa Gwamna shawara a Basic Education, Dr Hauwa Mustapha Babura da mataimaki na musamman ga Gwamna a fannin ilimin manya, Alhaji Garba Makama Gwaram sun yabawa Gwamna Namadi bisa kokarin sa na tallafawa shirin da sauran shirye-shiryen da hukumar bunkasa ilimin manya ke gudanarwa don baiwa daliban da suka fadi a jarrabawa damar sanin makamar da za su sami damar sake yin wata jarrabawar.

Sun kuma yi kira ga Jami’an da zasu gudanar da shirin da su saka tsoron Allah da kishin taimakawa daliban don cimma nasarar da aka sa a gaba.

Kazalika, sun yabawa kokarin Baban sakataren gudanarwa na hukumar Dr Abbas A Abbas bisa jajircewar sa wajen habaka ilimin manya a fadin jihar Jigawa.

Radio Nigeria ya bamu rahoton cewar, a lokacin taron an gudanar da takardu daban-daban a kan sabbin dabarun da za’a bi don tallafawa daliban da basu damar sake rubuta jarrabawar musamman a fannin turanci da lissafi da kuma shawarwariin da za ayi amfani dssu don kwalliya ta biya kufin sabulu.

Fiye da jami’ai masu hiror da dalibai 131 ne da aka gayyata daga kananan hukumomi 26 suka halarci taron da aka gudanar a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake cikin sakatariyar jihar jigawa.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025
  • Hukumar Alhazai Ta Jigawa Za Ta Shirya Taron Bita Na Musamman Ga Jami’anta
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya
  • SEMA Jigawa Da NEMA Da UNICEF Sun Bada Horo Akan Agajin Gaggawa A Auyo
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya