An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna
Published: 4th, August 2025 GMT
Sojoji sun kama wani gungun dillalan miyagun ƙwayoyi 28 a cikin Babban Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna.
Dilolin ƙwayar da aka kama sun haɗa da mata 11 da maza 18, lamarin da ya haifar da fargaba gane da yaɗuwar ɗabi’ar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a tsakanin iyalan sojoji da fararen hula da ke makwabtaka da su.
Kakakin Cibiyar Horas da Mayaƙan Ƙasa da aka barikin, Kyaftin Olusegun Abioye, ya bayyana cewa sojoji sun gano cibiyar dilolin ƙwayar ne a unguwanni Railway da Unguwar Lauya da ke cikin harabar barikin na Jaji.
Ya ƙara da cewa an kama shugabannin masu fataucin miyagun ƙwayoyi guda aƙalla guda 15 a waɗannan unguwanni biyu, kuma an miƙa duk waɗanda aka kama ga Hukumar Yaƙi da Ta’ammali da Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA).
NAJERIYA A YAU: Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a TarabaYa bayyana haka ne a yayin rangadin da ya jagoranci manema labarai yana mai ƙaryata labaran da ke cewa sojoji sun rusa unguwannin biyu.
Kyaftin Olusegun Abioye ya ƙara da cewa duk da cewa yankunan irinsu Unguwar Alasan da Unguwar da Unguwar Alhaji da Unguwar Aboki, da ke cikin harabar barikin suna taimaka wa sojoji da wasu ayyuka; amma duk da haka suna addabar al’ummar barikin sojojin da wasu matsaloli.
Ya bayyana cewa unguwanni sun riga sun haɗe da barikin sojojin wanda babbar cibiyar horon soji ce, kuma kusancin nasu kan jefa mazaunansu cikin mummunan haɗari a lokacin da sojoji ke atisayen amfani manyan makamai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barikin sojoji Dillalan ƙwaya ƙwayoyi Unguwar Lauya barikin sojoji
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa
Akalla ’yan gudun hijira miliyan daya da dubu 400 da ke Arewa maso gabashin Najeriya ne suke fuskantar barazanar yunwa bayan yanje tallafin da Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ke bayarwa.
Wani rahoton majalisar a kan abinci da tsaro wanda gwamnatin Najeriya, Shirin Kula da Abinci na Majalisar (FAO) da sauran masu ruwa da tsaki a baya dai sun yi hasashen ’yan Najeriya miliyan 33.1 za su iya fuskantar matsanancin karancin abinci daga tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2025.
Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawulHakan dai na nufin a yanzu yan kasar miliyan 34.7 ne ke nan suke cikin barazanar yunwar.
Ofishin Majalisar mai kula da Agaji (UNOCHA), a rahotonsa na mai taken “Najeriya a 2025 bukatun agajinta da kuma hanyoyin magance su” ya yi bayani daki-daki kan kalubalen da ake fuskanta a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe.
Rahoton ya ce akwai akalla yara miliyan daya da dubu 800 da kef ama da matsanancin karancin abinci.
Rahoton ya alakanta hakan da ci gaba da karuwar farashin kayayyaki a Najeriya wanda ya kai kaso 40.9 cikin 100 a watan Yunin 2024.
Kazalika, karuwar adadin na da nasaba da rage tallafin da MDD ke bayarwa ba, sanadiyyar yanke mata kudaden tallafin da musamman Amurka ke bayarwa.