Shirin Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa (MNCH) a Karamar Hukumar Gwarzo ta Jihar Kano ya samu gagarumar nasara, inda mata da yara da dama suka amfana da ayyukan kiwon lafiya kyauta iri-iri.

Wannan kamfen na mako guda, wanda Gwamnatin Jihar Kano tare da haɗin gwiwar UNICEF da sauran abokan hulɗa suka tallafa masa, na da nufin inganta lafiyar mata da yara tare da rage mace-macen da za a iya kauce wa ta hanyar samar da dama ga ayyukan kiwon lafiya.

Cibiyoyin lafiya a fadin karamar hukumar, ciki har da Asibitin Gwamnati na Gwarzo da Asibitin ‘Yar Kasuwa, sun bayar da rigakafi kyauta, shawarwari kan abinci mai gina jiki, kulawar haihuwa da sauran muhimman ayyuka na kiwon lafiya.

Jami’in Lafiya a matakin farko na karamar hukumar Gwarzo, Alhaji Sulaiman Abdulqadir Karaye, ya bayyana cewa gwamnatin jiha ta tabbatar da samuwar ingantattun magunguna da kayan aiki.

Ya shawarci mata da masu kula da yara su rika amfana da irin waɗannan damar ta hanyar ziyartar cibiyar kiwon lafiya mafi kusa domin samun ayyuka kyauta.

“Gwamnatin Kano ta bai wa fannin kiwon lafiya muhimmanci ta hanyar tallafi na baya-bayan nan da suka haɗa da na’urar sanyaya allurar rigakafi, janareto da sauran kayan aiki masu muhimmanci,” in ji shi.

Shugaban Asibitin ‘Yar Kasuwa kuma wakilin al’umma a Gwarzo, Salisu Ibrahim, ya bayyana jin daɗinsa kan yawan halartar jama’a.

Ya ce mazauna yankin sun fito sosai domin amfana da ayyukan da aka tanada.

A nata jawabin, jami’ar da ke kula da shirye-shiryen MNCH a karamar hukumar, Hajiya Amina Ado, ta bayyana cewa an gudanar da shirin lafiya cikin nasara a manyan cibiyoyin lafiya tare da wadatattun ma’aikata da kayan aiki.

Ta tabbatar da cewa mata da dama sun halarta, kuma ta yabawa haɗin gwiwar da ke tsakanin masu ruwa da tsaki.

Ɗaya daga cikin masu amfana a Asibitin ‘Yar Kasuwa, Shamsiyya Abubakar, ta yaba wa gwamnatin jiha da ta ƙaramar hukuma bisa samar da magunguna kyauta, inda ta bayyana shirin a matsayin ceton rai ga mata da dama a yankin.

Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa a Jihar Kano na da nufin kai ayyukan lafiya zuwa yankunan da ke da karancin samun kulawa, tare da rage gibin da ke tsakanin mata da yara wajen samun ingantacciyar kulawa.

 

Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kiwon Lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

A cewar sanarwar, AIHS za ta taimaka wajen haɓaka tambarin dangote da haɓaka dabarun haɗin gwiwa tare da masu ruwa da tsaki.

Kodinetan shirin Barista Festus Adebayo ya shaida wa manema labarai cewa, za a iya cike giɓin gidaje a ƙasar ta hanyar haɗin gwiwar Haɗin kan Jama’a masu zaman kansu (PPP).

Ya ce: “Kwarewa da haɗin gwiwa su ne manyan abubuwan da muka a gaba, idan aka yi la’akari da saurin ci gaban fasaha a cikin gine-ginen gidaje, samar da kudaɗe da kuma inganta tsarin.”

Ya ce taken taron na wannan shekara, Maimaita Gidaje Ta Hanyar Sabuntawa, wanda daidai yake da ainihin darajar kamfanin.

Barista Adebayo ya ce yana da ƙwarin gwiwar cewa haɗin gwiwa da kamfanin Simintin dangote zai taimaka wajen magance matsalar ƙarancin gidaje a ƙasar.

Ya ce sama da kashi 82 cikin 100 na mahalartan suna riƙe da matsayi na yanke shawara, tare da tabbatar da masu hulda kai tsaye tare da mutanen da ke da ikon saye.

Idan dai za a iya tunawa, Cibiyar Gine-gine ta Nijeriya (NIOB) da masu ruwa da tsaki a harkar gidaje sun bayyana kamfanin dangote a matsayin daya daga cikin manyan hanyoyin bunƙasa gidaje a Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sace jariri sabuwar haihuwa a asibitin Ekiti
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
  • Mai Martaba Sarkin Dutse Ya Kaddamar Da Rabon Zakka Ta Shekarar 1446
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa