Shirin Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa (MNCH) a Karamar Hukumar Gwarzo ta Jihar Kano ya samu gagarumar nasara, inda mata da yara da dama suka amfana da ayyukan kiwon lafiya kyauta iri-iri.

Wannan kamfen na mako guda, wanda Gwamnatin Jihar Kano tare da haɗin gwiwar UNICEF da sauran abokan hulɗa suka tallafa masa, na da nufin inganta lafiyar mata da yara tare da rage mace-macen da za a iya kauce wa ta hanyar samar da dama ga ayyukan kiwon lafiya.

Cibiyoyin lafiya a fadin karamar hukumar, ciki har da Asibitin Gwamnati na Gwarzo da Asibitin ‘Yar Kasuwa, sun bayar da rigakafi kyauta, shawarwari kan abinci mai gina jiki, kulawar haihuwa da sauran muhimman ayyuka na kiwon lafiya.

Jami’in Lafiya a matakin farko na karamar hukumar Gwarzo, Alhaji Sulaiman Abdulqadir Karaye, ya bayyana cewa gwamnatin jiha ta tabbatar da samuwar ingantattun magunguna da kayan aiki.

Ya shawarci mata da masu kula da yara su rika amfana da irin waɗannan damar ta hanyar ziyartar cibiyar kiwon lafiya mafi kusa domin samun ayyuka kyauta.

“Gwamnatin Kano ta bai wa fannin kiwon lafiya muhimmanci ta hanyar tallafi na baya-bayan nan da suka haɗa da na’urar sanyaya allurar rigakafi, janareto da sauran kayan aiki masu muhimmanci,” in ji shi.

Shugaban Asibitin ‘Yar Kasuwa kuma wakilin al’umma a Gwarzo, Salisu Ibrahim, ya bayyana jin daɗinsa kan yawan halartar jama’a.

Ya ce mazauna yankin sun fito sosai domin amfana da ayyukan da aka tanada.

A nata jawabin, jami’ar da ke kula da shirye-shiryen MNCH a karamar hukumar, Hajiya Amina Ado, ta bayyana cewa an gudanar da shirin lafiya cikin nasara a manyan cibiyoyin lafiya tare da wadatattun ma’aikata da kayan aiki.

Ta tabbatar da cewa mata da dama sun halarta, kuma ta yabawa haɗin gwiwar da ke tsakanin masu ruwa da tsaki.

Ɗaya daga cikin masu amfana a Asibitin ‘Yar Kasuwa, Shamsiyya Abubakar, ta yaba wa gwamnatin jiha da ta ƙaramar hukuma bisa samar da magunguna kyauta, inda ta bayyana shirin a matsayin ceton rai ga mata da dama a yankin.

Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa a Jihar Kano na da nufin kai ayyukan lafiya zuwa yankunan da ke da karancin samun kulawa, tare da rage gibin da ke tsakanin mata da yara wajen samun ingantacciyar kulawa.

 

Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kiwon Lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Wata kotu da ke birnin Madrid ta yi watsi da ƙarar da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Turai UEFA, LaLiga da Hukumar Kwallon Kafa ta Sipaniya suka shigar kan ƙin amincewa da gasar Super League.

Wannan yana nufin yanzu Real Madrid da sauran ƙungiyyoyin za su iya neman diyyar kudi Euro Milyan 4.

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 

Real Madrid ta ce, wannan hukuncin ya tabbatar da cewa UEFA ta karya dokokin gasa, kuma ƙungiyyoyi sun rasa maƙuden kuɗaɗe tun daga lokacin da aka dakatar da gasar.

Gasar wacce aka shirya farawa a shekarar 2021 tare da manyan ƙungiyoyin Turai, an yi hasashen zata samar da kusan Yuro miliyan 200 ga ƙungiyoyin da suka shiga.

A nata martanin hukumar UEFA ta dage cewa wannan sabon hukuncin ba ya nufin an dawo ko an amince da a buga gasar Super League ba ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare