Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
Published: 4th, August 2025 GMT
Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya bayar da umarnin bude jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida Lapai domin fara gudanar da karatu na yau da kullun.
Umurnin sake bude jami’ar ya biyo bayan nazari sosai kan matakan tsaro da inganta ababen more rayuwa a jami’ar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Neja Alhaji Abubakar Usman ya rabawa manema labarai ta hannun jami’in yada labaran sa Lawal Tanko a Minna.
Ya ce Gwamna Bago ya gamsu da ingantaccen gine-ginen tsaro da ci gaban ababen more rayuwa da aka yi don kare dalibai da ma’aikata da kuma al’ummar Jami’ar.
Sakataren Gwamnan Jihar Neja dai ya jaddada jajircewar Gwamnati wajen kare jin dadin dalibai da ma’aikata tare da tabbatar da ci gaban ilimi ba tare da katsewa ba.
Alhaji Abubakar Usman ya yaba da kokarin hadin gwiwa da jami’an tsaro da hukumomin jami’ar da shugabannin al’umma ke yi wajen magance kalubalen da ya kai ga rufe jami’ar.
A cewarsa, “Gwamna Bago, yayin da yake amincewa da sake bude taron, ya jaddada cewa, tsaro da jin dadin dalibai da ma’aikata su ne babban fifiko ga gwamnatinsa, ya kuma jaddada kudirinsa na inganta ilimi a matsayin ginshikin ci gaba, tare da tabbatar wa al’ummar Jami’ar goyon bayan gwamnati”.
Sanarwar ta yi kira ga daukacin dalibai da ma’aikatan da suka dawo da su bi ka’idojin tsaro da kuma bayar da cikakken hadin kai ga mahukuntan Jami’ar domin a sami zaman lafiya.
An rufe jami’ar na wani dan lokaci ne saboda matsalar tsaro da kuma asarar rayuka da aka yi a tsakanin al’ummar jami’ar, wanda a yanzu ake sa ran za a ci gaba da aiki a yau Litinin 4 ga watan Agusta ashirin da biyar.
ALIYU LAWAL
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
Hukumar Tattara Haraji ta Ƙasa (FIRS) ta ce ma’aikatanta hudu sun mutu a gobarar da ta tashi a ginin Afriland Towers da ke titin Broad da ke Legas, a ranar Talata.
Aminiya ta rawaito yadda gobara ta mamaye ginin da ke dauke da banki, hukumomi da wasu kamfanoni.
Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Laraba, mai magana da yawun Shugaban FIRS, Zaach Adedeji, wato Dare Adekanmbi, ya ce hukumar na cikin jimami da alhini kan rasuwar ma’aikatan nata.
Sanarwar ta ce, “Cike da alhini da bakin ciki, FIRS na sanar da rasuwar ma’aikatanta hudu a gobarar da ta tashi a ginin Afriland Towers da ke titin Broad, Legas, a ranar Talata. FIRS na daya daga cikin masu haya a ginin, inda Ofishin Binciken Matsakaicin Haraji da Ofishin Haraji na Onikan ke a bene na shida da na bakwai.”
“Jami’an tsaro da na kula da lafiya na hukumar sun gaggauta tuntubar hukumar kashe gobara lokacin da aka sanar da su. Amma da suka isa wurin, hayaki mai kauri da duhu ya turnuke ginin.”
“Hukumar da dukkan ma’aikatanta na cikin alhini kan wannan lamari. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka rasu, kuma muna tare da su a wannan lokaci mai wahala. Za mu ba su dukkan goyon baya da tallafi da ake bukata.”
“Muna aiki tare da dukkan hukumomin da suka dace a Legas domin gano musabbabin wannan mummunan al’amari. A yayin da ake ci gaba da bincike, za mu duba matakan kiyaye lafiyar dukkan ofisoshin FIRS da ke fadin ƙasa, ko na haya ne ko wanda ta mallaka.”