Aminiya:
2025-08-04@10:43:18 GMT

Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura

Published: 4th, August 2025 GMT

Amincewar Gwamnatin Tarayya da kashe Naira biliyan 712 biliyan don gyaran Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas ya haifar da ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya.

Wannan gagarumin kashe kuɗi, da Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da shi a ranar Alhamis da ta gabata, ya sanya masana harkar jiragen sama, ’yan adawa, da kuma jama’ar ƙasa yin tambayoyi game da buƙatarsa, tsadarsa, da kuma inda za a samo kuɗin.

Masu suka suna nuna yadda kuɗin ya yi yawa, har ya ninka kuɗin da aka ware wa Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama a kasafin kuɗin 2025 har sau goma. Hasali ma aikin ba ya cikin kasafin 2025.

Wannan ya sa wasu ke kiran aikin a matsayin “almubazaranci,” musamman ganin halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki.

Wani babban abin da ke haifar da surutan shi ne tsarin samo kuɗin. Gwamnati ta sanar da cewa za a samu kuɗin ne daga Asusun Ayyukan Raya Kasa na Renewed Hope Infrastructure Development Fund.

Amma jam’iyyun adawa, ciki har da ADC, sun ce Majalisar Dokoki ta Ƙasa ba ta amince da wannan kashe kuɗi ba, don haka suka kira shi “kashe kuɗi ba tare da kasafi ba.”

Yunkurinmu na jin ta bakin kakakin Majalisar Dattawa da ta Wakilai ya ci tura, wanda hakan ya ƙara ɓoye sirrin aikin.

Gyaran tashar jirgin ta Legas, wanda aka ba kamfanin gine-gine na CCECC kwangilar, zai haɗa da kwance ginin gaba ɗaya sannan a sake gina sabbin na’urorin zamani da tsarin lantarki da ruwa.

Wasu ayyukan sun haɗa da kwangilar Naira biliyan 44.13 na sabbin fitilun titin jirgin, Naira biliyan 24.27 na faɗaɗa wuraren ajiye jiragen sama, da kuma shingen tsaro . mai ɗauke da na’urorin zamani na Naira biliyan 49.9.

Jimillar kuɗin ta kuma haɗa da irin waɗannan gyare-gyaren a filayen jiragen sama na Kano da Fatakwal.

Wannan ba shi ne yunkurin farko na gyara filin jirgin na Legas ba. Tsohuwar gwamnatin Marigayi Muhammadu Buhari ta buɗe wani sabon tashar jirgin a shekarar 2022, wanda aka gina da kuɗin rancen dala miliyan 500 daga ƙasar China.

Amma wannan tashar ta fuskanci matsaloli masu yawa, inda kamfanonin jiragen sama da yawa suka ƙi amfani da ita saboda ƙarancin wurin ajiye manyan jirage.

Sabuwar tashar ta kasance ba a amfani da ita na tsawon fiye da shekara guda, inda yawancin kamfanonin jiragen sama na duniya ke ci gaba da amfani da tsohuwar tashar da yanzu aka shirya wa gagarumin gyara.

Yayin da gwamnati ke ci gaba da shirin ta, cece-kucen ya ƙara ta’azzara.

Tare da rashin samun cikakken bayani daga hukumomin Majalisar Dokoki da kuma tarihin ayyukan filayen jiragen sama da suka tsaya, jama’a na ci gaba da shakkar gaskiyar kuɗin da za a kashe da kuma nasarar da za a samu a wannan sabon aiki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kuɗaɗe Naira biliyan jiragen sama

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli

Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatar da kudurinta na yaki da zaizayar ƙasa, ambaliyar ruwa, da sauran matsalolin da suka shafi muhalli.

Wannan bayani ya fito ne daga Gwamna Abba Kabir Yusuf yayin kaddamar da babban shirin dashen itatuwa da za a shuka tsirrai miliyan biyar da rabi a faɗin jihar, wanda aka gudanar a ƙaramar hukumar Makoda.

Ya bayyana cewa babban burin wannan shiri shi ne magance dimbin matsalolin muhalli da ke addabar al’ummar Kano.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa waɗannan matsaloli sun jawo manyan kalubale ga al’umma.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta samar da dukkan kayayyakin da suka wajaba don kula da tsirran da za a dasa, domin su girma yadda ya kamata tare da cika manufarsu. Wannan goyon baya na da matuƙar muhimmanci wajen nasarar shirin.

Ya bukaci dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, sarakuna da jami’an raya al’umma da su shiga cikin wannan shiri, yana mai cewa halartar su na da matuƙar amfani wajen cimma burin da aka sa gaba.

“Idan aka kula da itatuwan da kyau, za su taka muhimmiyar rawa wajen rage sauyin yanayi da sauran matsalolin da suka shafi muhalli. Wannan na cikin manyan manufofin muhalli na Jihar Kano.” In ji shi.

Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yabawa Gwamna Yusuf bisa goyon bayan da yake bai wa ma’aikatar don yaki da matsalolin muhalli.

Wakilin Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II, wato Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, ya sake jaddada goyon bayan masarautar ga wannan shirin na dashen itatuwa.

A yayin taron, an gabatar da kyaututtuka ga wasu mutane da suka taka rawar gani wajen tallafawa al’ummominsu.

Wannan karramawa na matsayin kwarin gwiwa ne ga wasu domin su shiga irin waɗannan ayyuka na kula da muhalli.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri
  • Jamus ta soma jefa kayan agaji a Zirin Gaza
  • Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
  • Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya