Shugaba Bola Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata D’Tigress kyautar Dala dubu 100 da gidaje da lambar girmamawa ta OON, a matsayin karramawa bayan lashe kofin gasar ta bana.

Shugaban ya kuma ba masu horar da ’yan wasan dala 50,000 kowannensu.

Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan shugaban ya ’yan wasan ƙwallon ƙafa mata wata Super Falcons makamanciyar wannan kyautar ta dala 100,000 da lambar girma.

A wannan Litinin din ce tawagar ’yan wasan ƙwallon kwando ta mata ta Nijeriya ta koma ƙasar bayan lashe gasar ƙwallon kwando ta mata ta Afirka, wato Afrobasket.

Tawagar ta D’Tigress ta samu gagarumar tarba daga masoya ƙwallon kwando a Nijeriya, lokacin da suka sauka a filin jirgin sama na Abuja.

Ministar Mata Iman Sulaiman Ibrahim da takwararta ta al’adu, Hannatu Musawa ne suka yi wa tagawar rakiya tun daga birnin Abidjan zuwa Abuja.

A ranar Lahadi ne tawagar D’Tigress ta lashe gasar ƙwallon kwando ta mata ta Afirka, bayan doke Mali da ci 78-64 da aka fafata a Ivory Coast.

Wannan ne karo na bakwai da tawagar Nijeriya ta lashe kofin gasar a tarihi, wanda kuma shi ne na biyar a jere da ta ɗauka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ƙwallon kwando yan wasan ƙwallon ƙwallon kwando

এছাড়াও পড়ুন:

Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai 

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce idan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC suka sake lashe zaɓe a 2027, hakan zai lalata makomar ’yan Najeriya.

El-Rufai, ya faɗi haka ne a Jihar Sakkwato yayin wani gangamin wayar da kan jama’a da jam’iyyar adawa ta ADC, ta shirya.

Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba

Ya ce yana goyon bayan wannan haɗaka, kuma zai taimaka wajen ganin ’yan Najeriya sun sauke APC daga kan mulki.

“Idan muka bar wannan gwamnati ta ci gaba da mulki zuwa karo na biyu, ragowar abin da ya rage na haɗin kai da amincewa tsakanin ‘yan Najeriya zai lalace.

“Ƙasar na iya fuskantar barazana,” in ji shi.

“Wannan dai ta zama gwagwarmaya don ceto rayuwarmu.”

El-Rufai, ya ce dawowarsa siyasa ba don wata riba ko matsayi ba ne, sai don yana ganin gwamnatin yanzu ta gaza.

“Ba don ƙashin kaina nake wannan ba. Na dawo siyasa ne domin na yi wa al’umma hidima. Idan gwamnati ba ta cika alƙawari ba, dole ne na fito na faɗi gaskiya kuma na ɗauki mataki,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa haɗakar ADC an kafa ta ne domin yaƙar manufofin APC.

Ya ce gangamin da aka yi a Sakkwato shi ne farkon matakin neman goyon bayan jama’a a faɗin ƙasar nan.

El-Rufai, wanda ya ɗaya ne daga cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar APC, ya fice daga jam’iyyar a watan Maris, 2025.

Ya koma jam’iyyar SDP, saboda rashin jin daɗin yadda ake tafiyar da mulki a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
  • Ƴan matan Najeriya Sun Lashe Gasar Kwallon Kwando Ta Afirka
  • Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
  • Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai 
  • Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?
  • Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
  • Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10
  • Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
  • ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye