An yi wa Jalo Daudu sarautar Tafarkin Gombe
Published: 3rd, August 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dakta Abubakar Shehu Abubakar III, ya naɗa Dakta Ibrahim Jalo Daudu sarautar Tafarkin Gombe.
Dakta Daudu, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Babban Sakatare na Tarayya da Kwamishinan Lafiya na farko a Jihar Gombe.
Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5 Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-RufaiDaga baya ya zama Shugaban Ma’aikata a Gwamnatin Jihar Gombe, sannan ya riƙe wasu manyan muƙamai a Fadar Shugaban Ƙasa.
Yanzu haka, shi ne Kwamishina a Hukumar Kula da Ayyukan Ma’aikata na Ƙasa, inda yake wakiltar Jihohin Adamawa, Gombe da Taraba.
Dakta Daudu ya fito ne daga gidan sarauta a Gombe, kuma kakansa shi ne Hakimin Gombe na farko bayan masarautar ta koma zuwa birnin Gombe a yanzu.
Har ila yau, shi ne Ɗan Masanin Funakaye.
Sarautar Tafarki na ɗaya daga cikin manyan sarautun gargajiya a ƙasar Hausa.
Ana bai wa ɗan Sarki ko babban ɗan uwansa sarautar, kuma zai dinga bai wa Sarki shawara ko gyara idan ya zama dole.
Mai riƙe da wannan sarauta yana da damar shiga fada kai-tsaye da bai wa Sarki da masarauta shawara.
Asalin sarautar Tafarki ta samo asali ne tun zamanin Hausa Bakwai, kuma an ce mutum na farko da aka bai wa wannan sarauta shi ne Musa, a lokacin Sarkin Katsina Umaru Dallaje.
Yayin da yake sanar da naɗin, Sarkin Gombe, ya bayyana Dakta Daudu a matsayin mutum mai ƙwarewa, kuma wannan ne ya sa ya dace da wannan matsayi domin bai wa masarautar shawara.
Dakta Daudu, ya nuna farin ciki da godiyarsa ga Sarkin Gombe da majalisarsa, inda ya ce zai yi amfani da wannan dama wajen yi wa al’umma hidima cikin gaskiya da riƙon amana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Naɗi Sarauta sarki Tafarkin Gombe
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.
Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.
Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.
A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.
“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.
Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.
Tinubu ya kuma yaba wa masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.
Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.
Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.
Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.
Daga Bello Wakili