Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
Published: 4th, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatar da kudurinta na yaki da zaizayar ƙasa, ambaliyar ruwa, da sauran matsalolin da suka shafi muhalli.
Wannan bayani ya fito ne daga Gwamna Abba Kabir Yusuf yayin kaddamar da babban shirin dashen itatuwa da za a shuka tsirrai miliyan biyar da rabi a faɗin jihar, wanda aka gudanar a ƙaramar hukumar Makoda.
Ya bayyana cewa babban burin wannan shiri shi ne magance dimbin matsalolin muhalli da ke addabar al’ummar Kano.
Gwamna Yusuf ya jaddada cewa waɗannan matsaloli sun jawo manyan kalubale ga al’umma.
Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta samar da dukkan kayayyakin da suka wajaba don kula da tsirran da za a dasa, domin su girma yadda ya kamata tare da cika manufarsu. Wannan goyon baya na da matuƙar muhimmanci wajen nasarar shirin.
Ya bukaci dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, sarakuna da jami’an raya al’umma da su shiga cikin wannan shiri, yana mai cewa halartar su na da matuƙar amfani wajen cimma burin da aka sa gaba.
“Idan aka kula da itatuwan da kyau, za su taka muhimmiyar rawa wajen rage sauyin yanayi da sauran matsalolin da suka shafi muhalli. Wannan na cikin manyan manufofin muhalli na Jihar Kano.” In ji shi.
Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yabawa Gwamna Yusuf bisa goyon bayan da yake bai wa ma’aikatar don yaki da matsalolin muhalli.
Wakilin Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II, wato Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, ya sake jaddada goyon bayan masarautar ga wannan shirin na dashen itatuwa.
A yayin taron, an gabatar da kyaututtuka ga wasu mutane da suka taka rawar gani wajen tallafawa al’ummominsu.
Wannan karramawa na matsayin kwarin gwiwa ne ga wasu domin su shiga irin waɗannan ayyuka na kula da muhalli.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Dashen Itatuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.