Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
Published: 4th, August 2025 GMT
Tawagar Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta kai ziyarar ta’aziyya ga sabon Sarkin Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a fadarsa.
Ziyarar ta biyo bayan rasuwar marigayi Sarkin Gusau, Dakta Ibrahim Bello, wanda aka yi ta murna da shi a bisa kyakkyawan jagoranci da kuma gudunmawar ci gaban masarautu da jihar Zamfara.
Hajiya Larai Musa Lawal, ta mika sakon ta’aziyyar uwargidan shugaban kasar ga iyalan gidan sarautar tare da addu’ar Allah ya jikansa da rahama.
Ta kuma mika sakon taya murna ga sabon sarkin, tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya mai cike da hikima da zaman lafiya da hadin kai.
A nasa jawabi, sabon Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, ya nuna jin dadinsa ga uwargidan bisa wannan ziyarar da ta kai da kuma ci gaba da bada goyon baya.
Ya bayyana ta a matsayin ‘yar uwa kuma ya gode wa Gwamna Dauda Lawal bisa amincewar da aka yi masa.
Sarkin ya yi alkawarin rike gadon mahaifinsa da ya rasu tare da yin shugabanci cikin kankan da kai da sadaukarwa.
Tawagar ta kuma ziyarci Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara kuma Sarkin Anka, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad, domin yi masa ta’aziyyar rasuwar marigayi Sarkin Gusau.
Alhaji Attahiru ya yabawa uwargidan gwamnan wannan karimcin, inda ya bayyana hakan a matsayin alamar hadin kai da mutunta cibiyoyin gargajiya.
AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ta aziya Sarkin Gusau
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.