Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
Published: 4th, August 2025 GMT
Tawagar Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta kai ziyarar ta’aziyya ga sabon Sarkin Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a fadarsa.
Ziyarar ta biyo bayan rasuwar marigayi Sarkin Gusau, Dakta Ibrahim Bello, wanda aka yi ta murna da shi a bisa kyakkyawan jagoranci da kuma gudunmawar ci gaban masarautu da jihar Zamfara.
Hajiya Larai Musa Lawal, ta mika sakon ta’aziyyar uwargidan shugaban kasar ga iyalan gidan sarautar tare da addu’ar Allah ya jikansa da rahama.
Ta kuma mika sakon taya murna ga sabon sarkin, tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya mai cike da hikima da zaman lafiya da hadin kai.
A nasa jawabi, sabon Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, ya nuna jin dadinsa ga uwargidan bisa wannan ziyarar da ta kai da kuma ci gaba da bada goyon baya.
Ya bayyana ta a matsayin ‘yar uwa kuma ya gode wa Gwamna Dauda Lawal bisa amincewar da aka yi masa.
Sarkin ya yi alkawarin rike gadon mahaifinsa da ya rasu tare da yin shugabanci cikin kankan da kai da sadaukarwa.
Tawagar ta kuma ziyarci Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara kuma Sarkin Anka, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad, domin yi masa ta’aziyyar rasuwar marigayi Sarkin Gusau.
Alhaji Attahiru ya yabawa uwargidan gwamnan wannan karimcin, inda ya bayyana hakan a matsayin alamar hadin kai da mutunta cibiyoyin gargajiya.
AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ta aziya Sarkin Gusau
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirinta na yaki da gurbacewar kasa, zaizayar kasa da sauran kalubalen muhalli.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin bikin kaddamar da wani katafaren shirin dashen itatuwa, inda za a dasa itatuwa miliyan 5 da rabi a fadin jihar, wanda aka gudanar a karamar hukumar Makoda.
Ya ce babban makasudin wannan shirin shi ne a magance dimbin kalubalen muhalli da ke addabar al’ummar jihar Kano.
Gwamna Yusuf ya jadadda cewa wadannan kalubalen na haifar da babbar matsala ga al’umma.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta bayar da duk wani tallafin da ya dace don shayar da ‘ya’yan itatuwan, ta yadda za su yi girma da kuma cim ma burin da aka yi niyya. Wannan tallafi yana da mahimmanci don nasarar shirin.
Ya bukaci dukkan shugabannin kananan hukumomi 44, shugabannin gargajiya, da jami’an ci gaban al’umma (CDOs) da su sanya hannu a cikin wannan shirin, inda ya ce shigar su na da matukar muhimmanci wajen cimma manufofin shirin.
“Idan aka kula da kyau itatuwan da aka dasa ta wannan shiri za su taka rawar gani wajen magance sauyin yanayi da batutuwan da ke da alaka da hakan. Hakan ya yi dai-dai da manyan manufofin jihar Kano.”
Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yaba da kudurin Gwamna Yusuf na tallafawa kokarin ma’aikatar wajen dakile matsalolin muhalli.
Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, wanda ya wakilci Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II ya jaddada goyon bayan Masarautar kan shirin dashen itatuwa.
Taron ya gabatar da bayar da kyautuka ga mutanen da suka bayar da gudunmawa sosai wajen tallafawa al’ummarsu.
Wannan amincewa yana aiki azaman abin ƙarfafawa ga wasu don shiga cikin ayyukan muhalli.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO