Matafiya sun maƙale bayan ruftawar gada a Taraba
Published: 3rd, April 2025 GMT
Masu ababen hawa da dama sun maƙale a gadar Namne da ta rufta daura da hanyar Jalingo zuwa Wukari a Ƙaramar hukumar Gassol ta Jihar Taraba sakamakon ruwan sama kamar da bakin ƙwarya a da aka yi ranar Laraba.
Ruwan sama ya kawar da gadar da aka gina ta wucin gadi a hanyar da aka yi ta taimakon kai don taimakawa matafiya a kan hanya.
Gadar taimakon kai da aka gina a madadin babbar gadar da ta rufta watanni bakwai da suka gabata, ta kasance hanyar shiga ga masu ababen hawa da ke bin hanyar.
Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas ne ya bayar da kwangilar sake gina gadar a watan da ya gabata amma har yanzu ba a kai ga kwangilar zuwa wurin ba.
Masu ababen hawa da ke bin hanyar Jalingo da Wukari, an tilasta musu karkata zuwa hanyar garin Garba-Chede da ke ƙaramar hukumar Bali domin ci gaba da tafiya.
Masu ababen hawa da suka maƙale a ranar Laraba sun bayyana rashin jin daɗinsu kan gazawar gwamnatin tarayya na sake gina gadar kafin damina ta fara.
Wani direban babbar mota mai suna Bello Adamu ya ce direbobi da masu ababen hawa ba su ji daɗin yadda ba a sake gina gadar cikin lokaci mai kyau ba, kuma yanzu damina ta fara kawar da gadar wucin gadi a madadin babbar gadar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Taraba Wukari ababen hawa da
এছাড়াও পড়ুন:
Bakaken Fatar Amruka Da Suke Yin Hijira Zuwa Afirka Suna Karuwa
Ana samun Karin bakaken fatar Amurka da suke baro kasar suna dawo wa nahiyar Afirka domin samun kyakkyawar rayuwa a cikinta.
Mafi yawancin bakaken fatar suna nuna rashin gamsuwarsu da yanayin tattalin arziki da kuma siyasa na Amukra da su ka taka rawa wajen sa su, daukar matakin komawa Afirka da can ne asalin kakanninsu.
Wani dan kasar Amurka da ya rika yawo a tsakanin kasashe mabanbanta na Afirka a karshe ya tare a kasar Kenya, ya bayyana yadda yake jin ya saje a cikin nahiyar Afirka fiye da a can Amurka.
Auston Holleman wanda ya shahara da wallafa sakwanni a You Tube ya kara da cewa; Dukkanin mutane a Afirka sun yi kama da juna, ba kamar acikin turai, ko yankin Latin ba. “
Holleman ya kuma bayyana cewa yanayin siyasar Amruka a halin yanzu ya sa kasar tana fada da duk duniya baki daya.
Tun a 2019 ne dai kasar Ghana ta kaddamar da wani shiri na jawo hankalin bakaken fata a ko’ina suke a duniya domin samun wurin zama a cikinta.
A shekarar 2024 Ghana din ta ba da izinin zaman ‘yan kasa ga bakaken fata 524,mafi yawancinsu daga kasar Amurka.
Tun bayan da kamfanonin bakaken fata na Amurka irin su Adilah su ka koma Ghana, an sami karuwar bakaken fatar da suke komawa can.