Aminiya:
2025-11-03@04:03:10 GMT

Ruwan sama ya lalata aƙalla gidaje 70 a Filato

Published: 3rd, April 2025 GMT

Sama da gidaje 70 ne suka lalace da rumfuma a wata guguwa da ta yi ɓarna a unguwar Mabudi, Sabon Gida, da sauran unguwanni a ƙaramar hukumar Langtang ta Kudu a Jihar Filato.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, mamakon ruwan sama da aka yi a daren Laraba, wanda ya biyo bayan ruwan sama, ya yi ɓarna matuƙa.

INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye Najeriya ta yi kuskuren barin Boko Haram ta yi ƙarfi — Muftwang

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa kimanin gidaje 70 ne rufinsu ya ɗaga, yayin da wasu gine-gine suka ruguje.

Nanbol Nanzing, wani mazaunin ɗaya daga cikin unguwar da lamarin ya shafa, ya koka da yadda lamarin ya faru tare da yin kira ga gwamnatin jihar ta tallafa.

Shugaban ƙaramar hukumar Langtang ta Kudu, Hon. Nanfa Nbin ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Mista Iliya Bako.

A cewar sanarwar, kwamitin bayar da agajin gaggawa na Ƙaramar hukumar Langtang ta Kudu, wanda shugaban Ƙaramar hukumar ya kafa, ya ziyarci gidajen da lamarin ya shafa domin jajantawa waɗanda lamarin ya shafa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: da lamarin ya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure