Aminiya:
2025-06-15@16:29:41 GMT

Ruwan sama ya lalata aƙalla gidaje 70 a Filato

Published: 3rd, April 2025 GMT

Sama da gidaje 70 ne suka lalace da rumfuma a wata guguwa da ta yi ɓarna a unguwar Mabudi, Sabon Gida, da sauran unguwanni a ƙaramar hukumar Langtang ta Kudu a Jihar Filato.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, mamakon ruwan sama da aka yi a daren Laraba, wanda ya biyo bayan ruwan sama, ya yi ɓarna matuƙa.

INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye Najeriya ta yi kuskuren barin Boko Haram ta yi ƙarfi — Muftwang

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa kimanin gidaje 70 ne rufinsu ya ɗaga, yayin da wasu gine-gine suka ruguje.

Nanbol Nanzing, wani mazaunin ɗaya daga cikin unguwar da lamarin ya shafa, ya koka da yadda lamarin ya faru tare da yin kira ga gwamnatin jihar ta tallafa.

Shugaban ƙaramar hukumar Langtang ta Kudu, Hon. Nanfa Nbin ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Mista Iliya Bako.

A cewar sanarwar, kwamitin bayar da agajin gaggawa na Ƙaramar hukumar Langtang ta Kudu, wanda shugaban Ƙaramar hukumar ya kafa, ya ziyarci gidajen da lamarin ya shafa domin jajantawa waɗanda lamarin ya shafa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: da lamarin ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Ya kuma bukaci da a ci gaba da hada hannu da masu ruwa da tsaki a fannin, musamman domin dakile kalubalen da ake fuskanta na rashin amfana da albarkatun da ke madatsar ruwan, musamman domin kara bunkasa fannin aikin noma da kuma kara samar da wadataccen abinci.

A nasu martanin daban-daban, wasu daga cikin manoman sun yi kira ga hukumar ta HJRBDA, da ta samar musu da Taraktocin noma a daminar bana da kuma lokacin noman rani.

Tawagar ta hukumar HJRBDA, ta ziyarci wuraren adana ruwa; ciki har da na Challawa, Dam din Gorge, wanda ke adana ruwa mai karfin tsawon zurfin mita miliyan 962 da Dam din Tiga, wanda ke iya adana ruwan da zurfinsa ya kai kimanin mita biliyan 1.968 da madatsar ruwan ta Ruwan Kanya da ke iya adana ruwan da ya kai zurfin mita miliyan 50.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna