Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
Published: 29th, July 2025 GMT
Gwamnatin kasar Faransa ta yi kakkausar suka tare da tofin Allah tsine kan harin ta’addancin da aka kai birnin Zahidan na kasar Iran
Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin ta’addancin birnin Zahidan na kasar Iran, tare da jaddada adawar kasarta kan duk wani harin ta’addanci da aka kai kan fararen hula.
Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta fitar da wata sanarwa inda ta ce, birnin Paris na matukar yin Allah wadai da harin ta’addanci da aka kai a birnin Zahidan na kasar Iran a ranar 26 ga watan Yuli, wanda ya yi sanadin mutuwar fararen hula da dama ciki har da uwa da kuma ‘yarta.
Sanarwar ta kara da cewa, “A yayin da take mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka mutu, suna fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata a wannan harin ta’addanci.”
Wani abin lura a nan shi ne cewa, a safiyar ranar Asabar 26 ga watan Yuli ne wasu ‘yan ta’adda suka kai hari kan ginin hukumar shari’a ta cibiyar birnin Zahidan, fadar mulkin lardin Sistan da Baluchestan a kudu maso gabashin kasar Iran, inda suka kashe da kuma jikkata wasu Iraniyawa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: na kasar Iran
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Yayin da gasar wasannin kasa da kasa ta shekarar 2025 ke karatowa, an gudanar da bikin karba, da kaddamar da fitilar gasar a Asabar din nan, a shahararren gidan adana kayan tarihi na Sanxingdui, dake birnin Chengdu na kasar Sin.
Kaddamar da fitilar gasar a yau, ya alamta fara kidayar kwanaki 12, gabanin bude gasar karo na 12, wadda za ta gudana tsakanin ranakun 7 zuwa 17 ga watan Agusta dake tafe. An tsara kewayawa da fitilar tsawon kilomita 11, a yankunan biranen Chengdu, da Deyang, da Meishan, kuma mutane 120 za su yi karba-karbar kewayawa da ita, wanda hakan ke alamta ruhin gasar da kyakkyawan zumuncin da take kullawa.
An ayyana ‘yar wasan motsa jiki Huang Zhangjiayang daga birnin Chengdu, wadda ta taimakawa kasar Sin lashe lambar zinari a wasan nuna fasahohin lankwasa jiki yayin gasar Olympics ta lokacin zafi a birnin Paris, a shekarar bara, a matsayin wadda za ta fara zagayawa da fitilar. Yayin da kwararren dan wasan kwallon tebur na kasar Sin Ma Long, zai kasance na karshe da zai kewaya da fitilar. An baiwa Ma Long wannan dama ne bisa kwarewarsa, da kuma nasarori masu yawa da ya cimma, a gasannin da ya wakilci kasar Sin a cikinsu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp