Aljeriya ta bukaci taron gaggawa a kwamitin tsaro kan Falasdinu
Published: 3rd, April 2025 GMT
Aljeriya ta kira taron gaggawa na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya domin tattauna halin da Falasdinu ke ciki.
Bayan karuwar laifuffukan da yahudawan sahyoniyawa da suke aikatawa a kisan gillar da suke yiwa Palastinawa a yankin zirin Gaza da kuma ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri da sojojin yahudawan sahyoniya suka yi a yammacin gabar kogin Jordan, Aljeriya ta bukaci gudanar da wani taron gaggawa na kwamitin sulhu kan halin da Falasdinu ke ciki.
Kasar Aljeriya ta ba da misali da karuwar hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan Falasdinawa da ta mamaye musamman a yankin zirin Gaza a matsayin dalilin bukatar gudanar da wannan zama. Sama da wata guda kenan da Gaza ke cikin wani mummunan yanayi, ana kashe jama’a ciki har da ma’aikatan agaji.
An kuma gabatar da wannan bukata bayan gano gawarwakin ma’aikatan agaji 15 da ma’aikatan jin kai da daukin gaggawa a Gaza wadanda ke da alaka da kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu, da kungiyar kare fararen hula ta Falasdinu, da kuma Majalisar Dinkin Duniya.
An kuma bayyana karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan sahayoniya mazauna Yammacin Kogin Jordan ke haifarwa a matsayin wani dalili na neman wannan taron gaggawa.
A zamansa na 58, Kwamitin Kare Hakkokin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas da wani kuduri kan halin da ake ciki na kare hakkin bil’adama a yankunan Falasdinawa da suka mamaye ciki har da gabashin birnin Kudus .
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, an amince da kudurin ne a ranar Laraba inda kasashe 27 suka amince, 4 suka nuna adawa, sannan kasashe 16 suka kaurace kada kuri’ar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: taron gaggawa Aljeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.
M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.
Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”
Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.
Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.
Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.