HausaTv:
2025-06-15@02:22:53 GMT

Aljeriya ta bukaci taron gaggawa a kwamitin tsaro kan Falasdinu

Published: 3rd, April 2025 GMT

Aljeriya ta kira taron gaggawa na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya domin tattauna halin da Falasdinu ke ciki.

Bayan karuwar laifuffukan da yahudawan sahyoniyawa da suke aikatawa a kisan gillar da suke yiwa Palastinawa a yankin zirin Gaza da kuma ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri da sojojin yahudawan sahyoniya suka yi a yammacin gabar kogin Jordan, Aljeriya ta bukaci gudanar da wani taron gaggawa na kwamitin sulhu kan halin da Falasdinu ke ciki.

Kasar Aljeriya ta ba da misali da karuwar hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan Falasdinawa da ta mamaye musamman a yankin zirin Gaza a matsayin dalilin bukatar gudanar da wannan zama. Sama da wata guda kenan da Gaza ke cikin wani mummunan yanayi, ana kashe jama’a ciki har da ma’aikatan agaji.

An kuma gabatar da  wannan bukata bayan gano gawarwakin ma’aikatan agaji 15 da ma’aikatan jin kai da daukin gaggawa a Gaza wadanda ke da alaka da kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu, da kungiyar kare fararen hula ta Falasdinu, da kuma Majalisar Dinkin Duniya.

An kuma bayyana karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan sahayoniya mazauna Yammacin Kogin Jordan ke haifarwa a matsayin wani dalili na neman wannan taron gaggawa.

A zamansa na 58, Kwamitin Kare Hakkokin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas da wani kuduri kan halin da ake ciki na kare hakkin bil’adama a yankunan Falasdinawa da suka mamaye ciki har da gabashin birnin Kudus .

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, an amince da kudurin ne a ranar Laraba inda kasashe 27 suka amince, 4 suka nuna adawa, sannan kasashe 16 suka kaurace kada kuri’ar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: taron gaggawa Aljeriya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Ya kuma tuna irin muhimmiyar rawar da Majalisar tarayya ta taka a lokuta masu sarƙaƙiya a tarihin Nijeriya, ciki har da daƙile shirin ƙara wa’adi na uku da kuma kafa “Dokar Bukata” lokacin rasuwar tsohon shugaban ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike