Aminiya:
2025-07-30@21:19:31 GMT

Jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya kama wuta a Legas

Published: 3rd, April 2025 GMT

An shiga firgici da safiyar Alhamis  ɗin nan, bayan wani kwale-kwale na kamfanin Lagos Ferry Services (LAGFERRY) ya kama da wuta a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, a Legas inda mutane da dama suka jikkata.

Majiyoyi sun ce tashin wutar ta haifar da wata babbar gobara da ta tashi daga injin jirgin ruwan.

Wutar ta bazu cikin masaukin fasinjoji da sauri ta kama wasu fasinjojin da ke ciki.

Ruwan sama ya lalata aƙalla gidaje 70 a Filato INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye

“Akwai wani babban abin fashewa daga ɓangaren injin jirgin wanda hakan ya haifar da gobara wadda ta laƙume jirgin.

Majiyar ta ƙara da cewa, “har yanzu ba a san abin da ya haddasa tashin wutar ba, amma ana ci gaba da gudanar da bincike”.

Da take tabbatar da faruwar lamarin, Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA), ta ce fasinjoji huɗu ne kawai suka samu raunuka daban-daban.

“Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA) ta tabbatar da wata gobara da ta tashi da misalin ƙarfe 6:45 na safiyar yau a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, ɗauke da jirgin LAGFERRY mai suna “Igbega Eko” da ke kan hanyarsa ta zuwa tsibirin Ɓictoria Island.

“Bayan samun kira na ɓacin rai, jami’an masu bayar da agajin gaggawa ta LASWA cikin hanzari suka tashi zuwa wurin, suna aiki tare da haɗin gwiwa tare da LAGFERRY, masu gudanar da aikin kwale-kwale da sauran masu ba da agajin farko don gudanar da lamarin yadda ya kamata.

Mun yi farin cikin bayar da rahoton cewa an kwashe dukkan fasinjoji da ma’aikatan da ke cikin jirgin cikin ƙoshin lafiya, kodayake fasinjoji huɗu sun samu raunuka kuma a halin yanzu suna samun kulawar jami’an kiwon lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: LASWA jirgin ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Bayanin da ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya yi a baya-bayan nan game da hasashe kan tattalin arzikin kasar Sin cikin shekaru biyar masu zuwa ya jawo hankalin duniya sosai. Kuma sakamkon binciken jin ra’ayoyin jama’a da CGTN na babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG ya yi a tsakanin masu bayyana ra’ayoyi 47,000 a kasashe 46 daga shekarar 2023 zuwa 2025, ya nuna jama’ar sun nuna yakini game da karfi da juriyar tattalin arzikin kasar Sin.

Binciken ya nuna cewa, yawancin masu bayyana ra’ayoyin daga sassan duniya suna da kyakkyawan fata ga tattalin arzikin kasar Sin wajen samun bunkasa mai kyau a dogon lokaci, inda amincewarsu ta kai kashi 74.7 bisa dari, da 81.3 bisa dari, da kuma 81.9 bisa dari cikin shekaru uku a jere.

Binciken da aka yi a bana ya kuma nuna cewa, masu bayyana ra’ayoyin suna da kwarin gwiwa game da samun damammaki masu kyau a kasuwar Sin a cikin yanayin kasa da kasa mai sarkakiya da tashe-tashen hankula. A cikinsu akwai kashi 79.8 bisa dari da suka bayyana cewa, babbar kasuwar Sin ta ba da muhimman damammaki ga kasashen da suke gudanar da kasuwanci a ciki.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta