Aminiya:
2025-06-15@07:09:56 GMT

Jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya kama wuta a Legas

Published: 3rd, April 2025 GMT

An shiga firgici da safiyar Alhamis  ɗin nan, bayan wani kwale-kwale na kamfanin Lagos Ferry Services (LAGFERRY) ya kama da wuta a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, a Legas inda mutane da dama suka jikkata.

Majiyoyi sun ce tashin wutar ta haifar da wata babbar gobara da ta tashi daga injin jirgin ruwan.

Wutar ta bazu cikin masaukin fasinjoji da sauri ta kama wasu fasinjojin da ke ciki.

Ruwan sama ya lalata aƙalla gidaje 70 a Filato INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye

“Akwai wani babban abin fashewa daga ɓangaren injin jirgin wanda hakan ya haifar da gobara wadda ta laƙume jirgin.

Majiyar ta ƙara da cewa, “har yanzu ba a san abin da ya haddasa tashin wutar ba, amma ana ci gaba da gudanar da bincike”.

Da take tabbatar da faruwar lamarin, Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA), ta ce fasinjoji huɗu ne kawai suka samu raunuka daban-daban.

“Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA) ta tabbatar da wata gobara da ta tashi da misalin ƙarfe 6:45 na safiyar yau a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, ɗauke da jirgin LAGFERRY mai suna “Igbega Eko” da ke kan hanyarsa ta zuwa tsibirin Ɓictoria Island.

“Bayan samun kira na ɓacin rai, jami’an masu bayar da agajin gaggawa ta LASWA cikin hanzari suka tashi zuwa wurin, suna aiki tare da haɗin gwiwa tare da LAGFERRY, masu gudanar da aikin kwale-kwale da sauran masu ba da agajin farko don gudanar da lamarin yadda ya kamata.

Mun yi farin cikin bayar da rahoton cewa an kwashe dukkan fasinjoji da ma’aikatan da ke cikin jirgin cikin ƙoshin lafiya, kodayake fasinjoji huɗu sun samu raunuka kuma a halin yanzu suna samun kulawar jami’an kiwon lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: LASWA jirgin ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Da yake magana kan muhimmancin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana, Idris ya ce wannan ba lokacin murna kaɗai ba ne, har ma lokaci ne na nazari kan cigaban ƙasar wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya da farfaɗowar tattalin arziki.

 

Ya bayyana cewa ana amfani da kuɗaɗen da aka tara daga cire tallafin man fetur wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ciki har da manyan tituna guda biyu da za su haura kilomita 1,700, waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci da haɗa yankuna daban-daban.

 

Ya ce: “Manufar ba wai haɗa yankuna ba ce kawai, amma samar da damarmakin tattalin arziki.

 

“Nijeriya na ƙoƙarin komawa kan sahihiyar hanyar ta. Tana sake zama ƙasa mai daraja a idon duniya.

 

“Martabar da Nijeriya ke da ita a baya tana dawowa sannu a hankali. Masu zuba jari suna samun ƙarin ƙwarin gwiwa a ƙasar.”

 

Ya ƙara da cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata sun wuce batun tattalin arziki kawai, domin suna gina tushe ne na cigaba mai ɗorewa, raba dama ga kowa, da ƙarfafa gaskiya da riƙon amana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas