Aminiya:
2025-09-18@08:25:39 GMT

Jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya kama wuta a Legas

Published: 3rd, April 2025 GMT

An shiga firgici da safiyar Alhamis  ɗin nan, bayan wani kwale-kwale na kamfanin Lagos Ferry Services (LAGFERRY) ya kama da wuta a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, a Legas inda mutane da dama suka jikkata.

Majiyoyi sun ce tashin wutar ta haifar da wata babbar gobara da ta tashi daga injin jirgin ruwan.

Wutar ta bazu cikin masaukin fasinjoji da sauri ta kama wasu fasinjojin da ke ciki.

Ruwan sama ya lalata aƙalla gidaje 70 a Filato INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye

“Akwai wani babban abin fashewa daga ɓangaren injin jirgin wanda hakan ya haifar da gobara wadda ta laƙume jirgin.

Majiyar ta ƙara da cewa, “har yanzu ba a san abin da ya haddasa tashin wutar ba, amma ana ci gaba da gudanar da bincike”.

Da take tabbatar da faruwar lamarin, Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA), ta ce fasinjoji huɗu ne kawai suka samu raunuka daban-daban.

“Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA) ta tabbatar da wata gobara da ta tashi da misalin ƙarfe 6:45 na safiyar yau a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, ɗauke da jirgin LAGFERRY mai suna “Igbega Eko” da ke kan hanyarsa ta zuwa tsibirin Ɓictoria Island.

“Bayan samun kira na ɓacin rai, jami’an masu bayar da agajin gaggawa ta LASWA cikin hanzari suka tashi zuwa wurin, suna aiki tare da haɗin gwiwa tare da LAGFERRY, masu gudanar da aikin kwale-kwale da sauran masu ba da agajin farko don gudanar da lamarin yadda ya kamata.

Mun yi farin cikin bayar da rahoton cewa an kwashe dukkan fasinjoji da ma’aikatan da ke cikin jirgin cikin ƙoshin lafiya, kodayake fasinjoji huɗu sun samu raunuka kuma a halin yanzu suna samun kulawar jami’an kiwon lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: LASWA jirgin ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin

Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.

Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.

Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II

“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.

Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.

Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.

Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.

Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren  ibada da gidajen marayu.

Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.

Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin