Aminiya:
2025-04-30@19:53:35 GMT

Jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya kama wuta a Legas

Published: 3rd, April 2025 GMT

An shiga firgici da safiyar Alhamis  ɗin nan, bayan wani kwale-kwale na kamfanin Lagos Ferry Services (LAGFERRY) ya kama da wuta a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, a Legas inda mutane da dama suka jikkata.

Majiyoyi sun ce tashin wutar ta haifar da wata babbar gobara da ta tashi daga injin jirgin ruwan.

Wutar ta bazu cikin masaukin fasinjoji da sauri ta kama wasu fasinjojin da ke ciki.

Ruwan sama ya lalata aƙalla gidaje 70 a Filato INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye

“Akwai wani babban abin fashewa daga ɓangaren injin jirgin wanda hakan ya haifar da gobara wadda ta laƙume jirgin.

Majiyar ta ƙara da cewa, “har yanzu ba a san abin da ya haddasa tashin wutar ba, amma ana ci gaba da gudanar da bincike”.

Da take tabbatar da faruwar lamarin, Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA), ta ce fasinjoji huɗu ne kawai suka samu raunuka daban-daban.

“Hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Jihar Legas (LASWA) ta tabbatar da wata gobara da ta tashi da misalin ƙarfe 6:45 na safiyar yau a tashar jirgin ruwa ta Ipakodo da ke Ikorodu, ɗauke da jirgin LAGFERRY mai suna “Igbega Eko” da ke kan hanyarsa ta zuwa tsibirin Ɓictoria Island.

“Bayan samun kira na ɓacin rai, jami’an masu bayar da agajin gaggawa ta LASWA cikin hanzari suka tashi zuwa wurin, suna aiki tare da haɗin gwiwa tare da LAGFERRY, masu gudanar da aikin kwale-kwale da sauran masu ba da agajin farko don gudanar da lamarin yadda ya kamata.

Mun yi farin cikin bayar da rahoton cewa an kwashe dukkan fasinjoji da ma’aikatan da ke cikin jirgin cikin ƙoshin lafiya, kodayake fasinjoji huɗu sun samu raunuka kuma a halin yanzu suna samun kulawar jami’an kiwon lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: LASWA jirgin ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae

Kakakin ma’aikatar sharia a nan JMI ya bada sanarwan cewa,ma’aikatar za ta bayyanawa mutanen sakamakon bincken da suka gudanar kuma suke ci gaba da yi, dangane da fashewa da kuma gobatar da ta tashi a tashar jiragen ruwa ta Shahid Rajaee a cikin yan kwanakin da suka gabata. .

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran, ya bayyana cewa, Asgar Jahangir  kakakin ma’aikatar sharia da kuma Zabihullah Khudayiyan shugaban hukumar bincike ta kasa, sun gudanar da taron hadin guiwa da yan jaridu da kafafen yada labarai na cikin gida da waje a safiyar, dangane da fashewa da kuma gobarar da ta biyo baya a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajaee.

Banda haka jami’an sun amsa tambayoyin yan jarida bayan jawabansu dangane da hatsarin wanda ya lakume rayukan mutane, fiye da 70 da kuma jikata wasu kimani dubu guda.

Kafin haka dai jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaee ya bada umurni ga ma’aikatun biyu su gudanar da cikekken bincike don gani musabbabin wannan hatsarin sannan idan akwai wadanda suka da hannu, ko sakaci a cikinsa, a bi tsarin da ake da shi don hukunta wadanda suke da laifi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae