Leadership News Hausa:
2025-06-10@00:11:35 GMT

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Published: 1st, June 2025 GMT

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Za ki samu fulawa kamar gwangwani uku, ki zuba a roba sannan ki zuba suga kamar babban cokali biyu, sai gishiri rabin karamin cokali sai yis babba cokali daya, sai ki zuba ruwan dumi kofi daya da rabi, ki kwaba shi ki jujjuya shi ko ina ya hade, ki dan bubbuga shi kamar na minti uku haka, daga nan sai ki rufe shi ki kai shi rana domin ya taso.

Sai ki hada miyar da za ki ci da shi

Ki samu alayyahi da tattasai da dan tumatur idan kina so da taruhu da man, albasa:

Ki soya manki da albasa sannan ki zuba kayan miyan wanda dama kin jajjaga su, ki soya sai ki zuba magi, gishiri, kori, sannan ki kawo namanki ki zuba ki jujjuya shi,

Idan suka soyu, bayan sun soyu sai ki kawo alayyahinki wanda dama kin yanka shi kin wanke shi ki zuba ki ci gaba da juyawa, idan suka hade jikinsu sai ki rufe ki bar shi ya dan yi minti biyar haka kafin nan alayyahun ya dahu. Ita wannan miyar ba’a samata ruwa. A ci dadi lafiya.

Sannan kwabun funkason ya tashi, sai ki dakko shi ki zuba baikin fauda ki bubbuga shi saboda iskar ta fita, sai ki dora mai a wuta, wasu suna fadada shi da hannu, wasu kuma suna samun murfin wani abu haka mai fadi su yi da shi ko filat haka su rika zubawa suna fadadawa sannan su jefashi a cikin mai, za ki ga yayi ja shin e ya soyu, sai ki juya saman shima ya soyu haka za ki yi har ki gama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Rannakun Bikin Babbar Salla

A rana ta biyu tabukuwan  babbar salla, sojojin HKI suna ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyasahi da kuma rusa matsugunansu a yankin Gaza.

A yau Asabar kadai gwamman Falasdinawa ne su ka yi shahada a cikin sansanonin da Falasdinawa suke gudun hijira a cikinsu.

An sami shahidai 5  da kuma wasu mutane  biyu da su ka jikkata a kusa da cibiyar rana kayan agaji a yammacin Rafah dake kudancin zirin Gaza.

A yammacin birnin Khan-Yunus kuwa wasu Faladinawa 12 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 40 su ka jikkata saboda harin da ‘yan sayahoniyar su ka kai wa sansaninsu.

A arewacin Khan-Yunus kuwa, sojojin mamayar sun ruguza gidajen Falasdinawa da dama.

A kusa da cibiyar kiwon lafiya ta ” Majma’u -Shifa” dake yammacin birnin Gaza, adadin shahidai ya kai 7 wasu biyu kuwa su ka jikkata.

Daga lokacin da HKI ta shelanta yaki akan mutanen Gaza a 2023, adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 54,677, yayin da wadanda su ka jikkata su ka kai 125,530.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC
  •  Kasar Rwanda Ta Fice Daga Cikin Kungiyar Tattalin Arziki Ta Tsakiyar  Afirka
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa
  • Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
  • Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa
  • HKI Ta Kashe Wani Babban A Cikin Shuwagabannin Falasdinawa
  • Magidanci ya shiga hannu kan kashe matarsa mai juna biyu da duka
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Rannakun Bikin Babbar Salla
  • Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027
  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma