Aminiya:
2025-10-15@19:05:53 GMT

Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda

Published: 15th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi sulhu da ’yan ta’adda ba waɗanda ke kashe mutane ba gaira ba dalili.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a yau a wajen bikin yaye sabbin jami’an tsaron cikin gida (Community Watch Corps – CWC) guda 100, a karo na uku da aka gudanar a Katsina.

Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Radda, ya karyata rahotannin da wasu kafafen yaɗa labarai suka yada cewa gwamnatinsa tana tattaunawa da ’yan bindigar da ke ɓoye a dazuka.

A cewarsa: “Babu wata tattaunawa ko sasanci da gwamnati ke yi da ’yan ta’adda. Wadannan labarai ƙarya ne, kuma manufar gwamnati ita ce kawo ƙarshen ta’addanci, ba yin sulhu ba.”

Sai dai ya ce, gwamnati za ta iya rungumar zaman lafiya idan waɗannan mutane sun yi tuba na gaskiya, tare da miƙa wuya, suka daina zubar da jini.

Gwamna Radda, ya bayyana cewa horar da jami’an CWC wani ɓangare ne na sabuwar dabarar gwamnati ta inganta tsaro, musamman a yankunan karkara da suka fi fama da hare-haren ’yan ta’adda.

Tun bayan ƙaddamar da Katsina jami’an tsaron a shekarar 2023, an horar da dubban matasa sama da 2,400 daga sassa daban-daban na jihar.

Wadannan jami’ai na aiki tare da ’yan sanda, sojoji, da jami’an Sibil Difens, don taimakawa wajen samun bayanan sirri da hana hare-haren ’yan ta’adda.

Gwamnan, ya ce horar da waɗannan jami’ai zai taimaka wajen kawo ƙarshen satar mutane da hare-haren ’yan bindiga, tare da tabbatar da zauna lafiya a Jihar Katsina.

Ya kuma yi kira ga al’umma su bai wajami’an tsaro haɗin kai, su rika bayar da bayanai domin ganin an samu nasara a yaki da ta’addanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamna Radda hare hare yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna

Sojoji sun kama wata mata da mijinta da suka yi kaurin suna wajen safarar makamai a yankin Saminaka da ke Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna.

Dubun ma’auratan ta cika ne a wani shingen binciken inda sojojin Rundunar Operation Fansan Yamma suka gano harsasai 1,207 hannunsu.

Kakakin rundunar, Manjo Samson Zhakom ya ce an kama su ne a hanyars ta kai wa ’yan ta’addan da ke addabar yankin Arewa maso Yamma makaman.

Ya ce matar mai shekaru 18 mijin masi shekaru 40 suna tsare suna amsa tambayoyi, yana mai jinjina wa sojoji da ’yan banga bisa kwarewar da suka nuna wajen kama miyagun.

Kofin Duniya: Da sauran rina a kaba duk da Najeriya ta ci Jamhuriyar Benin 4-0 Na yafe wa Maryam Sanda —Mahaifin Bilyaminu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna
  • ’Yan bindiga sun kai hari a Kankia
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya