Aminiya:
2025-12-01@17:05:02 GMT

Kaso 16 na ’yan Najeriya ne kawai ke da wajen wanke hannu — UNICEF

Published: 16th, October 2025 GMT

Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF), ya bayyana cewa kashi 16 cikin 100 na ’yan Najeriya ne kawai ke da wajen wanke hannu mai tsafta a gidajensu.

Wakiliyar UNICEF a Najeriya, Chisom Adimorah ce, ta bayyana haka a ranar Laraba yayin bikin Ranar Wanke Hannu ta Duniya ta 2025, wanda Ma’aikatar Ruwa da Tsaftar Muhalli ta Tarayya ta shirya.

DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba Ka da a ɗora wa Tinubu laifin rikicin da ke faruwa a PDP — Fayose

Adimorah, ta nuna damuwarta kan wannan matsala, inda ta ce duk mutane biyar cikin shida a Najeriya ba su da waje  da za su iya wanke hannunsu yadda ya kamata.

Ta yi kira ga gwamnati, ƙungiyoyi, kamfanoni da kuma ’yan ƙasa su haɗa kai wajen inganta tsaftar hannu a ƙasar.

Ta kuma tabbatar da cewa UNICEF za ta ci gaba da taimaka wa Najeriya wajen inganta manufofin tsaftace muhalli domin su dace da sabbin ƙa’idojin WHO da UNICEF kan tsaftar hannu.

Ministan Ruwa da Tsaftar Muhalli, Injiniya Joseph Utsev, ya bayyana muhimmancin wanke hannu wajen kare lafiyar jama’a, inda ya ce “wanke hannu na ceton rai tare da kariya daga barazana.”

Utsev, ya ƙara da cewa ‘Taswirar Najeriya ta Tsaftar Hannu’ wadda aka ƙaddamar a shekarar 2022, ita ce har yanzu ke jagorantar ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan wanke hannu a faɗin ƙasar nan.

Ya jaddada cewa dole ne a fara koyar da wanke hannu tun daga makarantar firamare domin yara su saba da wannan ɗabi’a tun suna ƙanana.

A nasa jawabin, Aghogho Gbetsere, wanda ya wakilci Ministan Muhalli, ya shawarci ’yan Najeriya su riƙa wanke hannunsu a kai a kai, inda ya ce hakan na iya rage hatsarin kamuwa da cututtukan gudawa da kashi 50 da kuma cututtukan da suka shafi numfashi da kashi 25.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya wanke hannu wanke hannu

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran

Rahotanni sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar Turkiya ya iso birnin Tehran a jiya lahadi kuma  ya samu kyakkyawar tarba daga takwaransa na kasar iran Abbas Araqchi.

Ziyarar tasa ana saran za ta kara fadada dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, ganin cewa dukkan kasashen biyu suna taka rawa a batutun da suka shafi yanki dama duniya baki daya.

Bugu da kari bayan ganawarsa da Araqchi da musayar ra’ayoyi kan batutuwa daban daban, zai gana da sauran manyan jami’an gwammnatin kasar, da ake saran za su tattauna kan alakar dake tsakaninsu da kuma irin ci gaban da aka samu a yankin da dai sauran batutuwa na kasa da kasa.

Ana sa bangaren shugaban kasar iran Masud pezeshkiyan a lokacin ganawarsa da Hakan fidan ministan harkokin wajen kasar turkiya ya jaddada game da muhimmancin hadin kan kasashen musulmi cikin gaggawa, yace ya kamata kasashen musulmi su rike duba yanayi da yan uwansu suke ciki, kuma a nisanci tsaurara alamura, adaidai lokacin da suke fuskantar matsin lamba daga kasashen waje.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Shugaban Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025  Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  • An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Turkiya
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo