Aminiya:
2025-12-01@19:09:35 GMT

Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC

Published: 16th, October 2025 GMT

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Joash Ojo Amupitan a matsayin sabon shugaban Hukumar zaɓen Najeriya mai zaman kanta INEC, bayan tantancewa.

Sabon shugaban Hukumar zaɓen Najeriya mai zaman kanta INEC, Joash Ojo Amupitan dai ya halarci zauren  Majalisar Dattawan Najeriya domin zaman tantance shi a yau Alhamis ne.

Amupitan ya halarci zauren Majalisar tare da rakiyar Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Ododo da wasu jami’an gwamnati.

Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano Kashi 16 na ’yan Najeriya ne kawai ke da wajen wanke hannu — UNICEF

Da misalin ƙarfe 12:50 na rana ne, mai baiwa shugaban Ƙasa shawara kan Harkokin Majalisar Dattawa (Majalisar Dattawa), Sanata Abubakar Lado ne ya shigar da sabon shugaban INEC zuwa zauren majalisar dattijai, kuma tuni ya zauna gabanin fara aikin tantance shi.

An bar Amupitan ya shiga zauren majalisar ne bayan shugaban masu rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele ya bayar da umarnin a samar da doka ta 12 domin ba wa baƙi damar shiga zauren majalisar, kuma shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Abba Moro ya mara masa baya.

Matakin na zuwa ne bayan Shugaba Tinubu ya aike wa majalisar wasiƙar buƙatar tantance shi.

A makon da ya gabata ne dai majalisar magabatan ƙasar ta amince da naɗin Farfesa Amupitan a matsayin wanda zai jagoranci hukumar zaɓen INEC.

Bayan tantancewa da amincewar majalisar dattawan, Shugaba Tinubu zai rantsar da shi a matsayin shugaban hukumar ta INEC.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Majalisar Dattawa Majalisar Dattawa zauren Majalisar zauren majalisar Majalisar da

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A mafi yawan ƙasashen duniya, ana ɗaukar jakadu a matsayin fuskar ƙasa kuma ginshiƙan hulɗar diflomasiyya. Saboda haka, akwai muhimman halaye da suke tilas jakadan ƙwarai ya mallaka domin ya wakilci ƙasarsa cikin mutunci, da nagarta da kwarewa.

 

Tun bayan da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fitar da sunayen jakadu da yake sa ran majalisar kasa ta tantance ne dai batun ke ta shan suka daga manazarta kan sunayen da ya fitar.

Ko wadanne irin halaye ya kamata jakada ya mallaka a yayin da za a tura shi a matsayin wakili a wata kasa?

NAJERIYA A YAU:Waiwaye Kan Irin Gudunmawar Da Sheikh Dahiru Bauci Ya Bayar Ga Cigaban Addini DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  •  Kasar Ireland Ta Sauya Sunan Shugaban  “Isra’ila” Da Na Shahidiyar Falasdinu
  • An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru  
  • Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa
  • Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila
  • Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32