Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina
Published: 16th, October 2025 GMT
Wani daga cikin waɗanda suka ji rauni, wanda shi ne mai kuɗin, ya gode wa jami’an FRSC bisa gaskiya da amana da suka nuna, yana mai cewa abin koyi ne ga kowa.
FRSC ta gargaɗi direbobi da su riƙa kula da motoccinsu akai-akai tare da bin ƙa’idojin hanya domin guje wa aukuwar haɗura.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wasu mutane shida da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke gudanar da ayyukansu a karamar hukumar Toro ta jihar tare da ceto wasu mutane uku da aka sace ba tare da komi ba.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), CSP Mohammed Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Bauchi.
A cewar sanarwar, rundunar ‘yan sandan ta samu kiran gaggawa daga wani dan banga da ke kauyen Euga da misalin karfe 12:01 na safiyar ranar 29 ga watan Satumba, 2025, inda ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi awon gaba da wasu mutane uku wato Idi Umar, Idi Lawan, da Musa Lawal.
Wakil ya ce “A martanin da aka mayar, an kaddamar da wani aiki na hadin gwiwa wanda ya hada da rundunar ‘yan sanda ta Toro, Toro Division, Nabordo Division, da kuma jami’an tsaro na cikin gida.”
Ya kara da cewa rundunar hadin guiwa ta bin diddigin wadanda ake zargin har zuwa wajen kauyen, inda suka gudanar da wani samame na dabara wanda ya kai ga ceto wadanda lamarin ya rutsa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi.
Wadanda aka kama sun hada da Abubakar Usman, Adamu Alo, Abubakar Aliyu, Umar Habu, Abubakar Mamman Abubakar, da Shehu Sambo.
Karshen/Alhassan.