An Bukaci Manoman Kano Su Shiga Baje Kolin Kayan Noma Na Kasa
Published: 16th, October 2025 GMT
Hukumar Noma da Raya Karkara ta Jihar Kano (KNARDA) ta yi kira ga manoma da masu ruwa da tsaki a harkar noma da masu kirkire-kirkire a jihar da su shiga baje kolin noma na kasa da ke tafe.
A cikin wata sanarwa da Sashen Kula da Ayyukan Yada Labarai, KNARDA ya fitar, ta bayyana taron a matsayin wani babban dandali na baje kolin kayayyakin amfanin gona, da fasahohin zamani, da ke inganta samar da abinci da raya karkara.
Hukumar ta ja hankalin daidaikun jama’a da kungiyoyi a Kano da su yi amfani da wannan damar wajen gabatar da nasarorin da suka samu da kuma gano sabbin hanyoyin kasuwanci a fannin noma.
KNARDA ta kuma jaddada aniyar ta na tallafawa kokarin da ke inganta ayyukan noman zamani da ci gaban karkara.
Abdullahi Jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.
Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA