Manyan malamai, shugabanni na addini, gargajiya da siyasa daga sassan Arewacin Najeriya sun hallara a Kaduna domin Taron Musamman na Malaman Arewa (Special Northern Ulamah Summit), wanda ya mayar da hankali kan nemo mafita ta dindindin ga matsalolin tsaro da ƙalubalen tattalin arziki da ke addabar yankin.

 

Taron ya tattauna kan ƙarfafa haɗin kai tsakanin malamai, amfani da kafafen sada zumunta ta hanyar da ta dace, da kuma ƙarfafa hulɗa tsakanin shugabannin addini, gargajiya da na siyasa domin dawo da zaman lafiya da daidaito a al’umma.

 

Da yake jawabi, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar na Uku, wanda Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli ya wakilta, ya kira malamai da shugabanni su haɗa kai wajen yaki da rashin tsaro, talauci da rarrabuwa. Ya gargaɗi malamai da al’umma da su guji amfani da kafafen sada zumunta wajen yada ƙarya da haifar da fitina.

 

Sarkin Musulmi ya jaddada cewa zaman lafiya da kwanciyar hankali za su tabbata ne kawai idan aka samu haɗin kai na gaskiya tsakanin sassa daban-daban na al’umma bisa koyarwar addinin Musulunci.

 

A jawabinsu na haɗin gwiwa, Sheikh Abdullahi Bala Lau da Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi sun bayyana cewa son kai, rarrabuwa, da matsin tattalin arziki na daga cikin manyan abubuwan da ke kawo rashin tsaro a Arewa. Sun ce lokaci ya yi da shugabannin addini, gargajiya da siyasa za su buɗe tattaunawa mai fa’ida tare da yin aiki tare domin kawo ƙarshen rikice-rikice da koma bayan tattalin arziki.

 

Haka kuma, Sanata Abdulaziz Yari Abubakar na Jihar Zamfara, Sanata Shehu Buba na Jihar Bauchi, da Honourable Alhassan Ado Doguwa na Jihar Kano, sun yaba da wannan taro suna mai cewa lokaci yayi da za a ɗauki mataki na haɗin kai domin ceto yankin Arewa daga ƙalubale.

 

Sanata Yari ya ce rashin tsaro na ci gaba da ƙaruwa ne saboda rashin daidaito da ƙarancin damar tattalin arziki, yayin da Sanata Buba ya jaddada muhimmancin ƙarfafa matasa da aiwatar da gyare-gyaren zamantakewa bisa ka’idojin Musulunci.

 

Honourable Doguwa, wanda shi ne Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Majalisar Wakilai na Arewa (Northern Caucus), ya tabbatar da goyon bayan majalisa ga sakamakon taron, tare da alkawarin haɗa hannu da hukumomi da shugabanni domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a yankin.

 

A ƙarshen taron, mahalarta sun amince da kafa Cibiyar Jagorancin Addinin Musulunci ta Ƙasa (National Islamic Leadership Forum), domin haɗa malamai, shugabanni da masu tsara manufofi a ƙarƙashin dandalin haɗin kai, zaman lafiya da ci gaba.

 

COV: Shettima Abdullahi

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Haɗin Kai Rarrabuwa Rashin Tsaro Taron

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kai hari a Kankia

Dandazon ’yan bindiga sun kai hari a yankin Kankia da ke Jihar Katsina inda suka halaka mutum daya tare da jikkata wasu da dama.

Shaidu sun ce ’yan bindiga kimanin 100 a kan babura ne suka kai harin a yankin Kwadawa da ke Gundumar Gashi da ke Karamar Hukumar Kankia, inda ake Ana zargin maharan sun kai harin daukar fansa ne,

Maharan da suka kai farmaki a yankin da ke Gabahsin karamar hukumar, sun sace dabbobi da ba a san adadinsu ba, suna masu barazanar halaka duk mutanen yankin.

Wakilinmu ya ruwaito cewa a halin yanzu mazauna yankunan Bogga, Taiba Badole, Arahiya, Kwandawa, Rumawa, Gangara da Rugar Bindo da ke gundumar Gachi da kuma Fakuwa/Kafindangi suna yin kaura domin tsira da rayuwarsu.

Ya kamata ‘yan fim su rika taimaka wa kananan cikinsu-Rukayya Abdullahi Juyin mulki: Shugaba Rajeolina ya tsere daga ya rushe majalisa

Wani ganau ya ce’yan bindigar suna kutsawa zuwa yankunan da a baya suke zauna cikin aminci, kmar Kankia , Charanchi, Kusada da a baya ba sa fama da matsalar tsaro.

Kazalika mazauna kauyukan Tama da Dokaji da ke Karamar Hukumar Bindawa sun bayyana fargabarsu da bayan samun labarin harin na Kankia,  mai makwabtaka da su.

Haladu Badole ya ce, “Kimanin kwanaki uku ke nan da muka lura da wasy bakin fuska a yankunanmu, kuma a daren jiya sun kai hari suka sace dabbobin mutane.”

Mazauna yankin sun yi kira ga hukumomi da su gaggauta tura jami’an tsaro zuwa yankin domin samar da tsaro.

A baya yankin Gabashin Karamar Hukumar Kankia ya kasance cikin amici duk da ’yan hare-haren da aka samu a yankunan Rimaye, Magam, Sukuntuni, Gyaza daKunduru da ke karamar hukumar.

Wakilinmu ya tuntubi kakakin ’yan sandan jihar, amma ya bayyana masa cewa suna gudanar da bincike domin gano hakikanin halin da ake ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 
  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma
  • Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Kungiyar NAM Su Hada Kai Don Fuskantar Rashin Bin Doka Da Oda A Duniya
  • Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki
  • Jihar Kwara Zata Haɗin Kai Da Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Horas Da Matasa Fasahar AI
  • Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kai hari a Kankia