Aminiya:
2025-10-15@16:21:22 GMT

Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP

Published: 15th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya fice daga jam’iyyar PDP.

Mai magana da yawun gwamnan, Daniel Alabrah, ne ya sanar da hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook na ainihi, kodayake bai bayyana dalilin ficewar gwamnan daga jam’iyyar ba.

Har ila yau, bai bayyana ko Gwamna Diri zai koma APC mai mulki ko kuma hadakar ’yan adawa ta ADC ba.

Aminiya ta gano cewa Gwamna Diri yana halartar wani taro da mambobin majalisar zartarwa ta jiha, inda ya bayyana musu wannan bayani.

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Bayelsa, Rt. Hon. Abraham Ingobere, yana cikin mahalarta taron.

A cikin sa’o’i kaɗan da suka gabata, Gwamna Diri tare da tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, sun halarci bikin ƙaddamar da otal ɗin Best Western Plus da ke Yenagoa.

Haka kuma, dukkan mambobin PDP da ke cikin Majalisar Dokokin Jihar da kuma Kwamishinoni a Majalisar Zartarwa ta Jiha sun fice daga jam’iyyar.

Gwamna Diri ya taɓa zama Kwamishina a gwamnatin PDP a lokacin da Goodluck Jonathan ke matsayin Gwamnan Jihar Bayelsa. Haka kuma, ya kasance Babban Sakataren Gwamna Seriake Dickson, wanda shi ne wanda ya gabace shi.

An zaɓi Diri a matsayin ɗan Majalisar Wakilai a shekarar 2015 a ƙarƙashin PDP, sannan a 2019 aka zaɓe shi a matsayin Sanata mai wakiltar Bayelsa ta Tsakiya.

A shekarar 2020 aka zaɓe shi a matsayin Gwamnan Jihar Bayelsa, kuma aka sake zaɓar shi a 2023, duka a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa daga jam iyyar Jihar Bayelsa Gwamna Diri

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

“Salon shugabancinsa da amincewa da cancanta sama da son rai ne ya sa kowane mai kishin ci gaba daga ƙarshe yake samun mafaka a APC,” in ji shi.

Gwamna Mbah ya bayyana shiga jam’iyyar APC bayan tattaunawa da magoya bayansa, yana mai cewa hakan “sabuwar tafiya ce” ga Jihar Enugu da yankin Kudu maso Gabas wajen samun babban matsayi a siyasar ƙasa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta October 14, 2025 Manyan Labarai Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato October 14, 2025 Siyasa PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
  • DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Kamaru: Jam’iyyun adawa sun ayyana Bakary a matsayin wanda ya lashe zaɓe
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye