Kwanturola na hukumar gyaran Hali a Najeriya reshen jihar Zamfara, Murtala Muhammad Haruna, ya yi kira da a shigar da fursunoni cikin tsarin inshorar lafiya na kasa (NHIS) domin tabbatar da samun ingantattun ayyukan kiwon lafiya.

 

Ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga kwamishiniyar lafiya ta jihar Zamfara, Dakta Nafisa Muhammad Maradun, a ofishinta da ke Gusau.

 

Haruna ya ce shirin ya yi dai-dai da hangen nesan babban kwamandan hukumar gyaran hali ta Najeriya da nufin inganta jin dadin fursunonin da ke gidajen yari.

 

Kwantirolan ya kuma jaddada bukatar inganta asibitin hukumar da ke cibiyar tsaro ta matsakaita, Gusau, da samar da isassun kayan aikin likita da magunguna masu mahimmanci don biyan bukatun kiwon lafiyar fursunoni.

 

Murtala Mohammed Haruna ya lura da cewa, matakin ya dace da ajandar sabunta bege na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda ya mayar da hankali kan inganta jin dadin daukacin ‘yan Najeriya, ciki har da wadanda ke tsare.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Mustapha Abubakar ya fitar, ya ce sun kai ziyarar ne da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumar gyaran hali da ma’aikatar lafiya ta jihar domin inganta harkokin kiwon lafiya ga fursunonin dake fadin jihar ta Zamfara.

 

Da take mayar da jawabi, Dakta Nafisat Muhammad Maradun ta yabawa hukumar gidan yari bisa jajircewar da take yi na kula da fursunonin da kuma kare lafiyar jama’a.

 

Ta bayyana cewa tuni Gwamna Dauda Lawal ya siyo kayayyakin jinya da kayan aikin da ya yi alkawari a ziyarar da ya kai gidan gyaran hali na Gusau.

 

A cewarta, nan ba da jimawa ba za a mika magungunan da aka sayo ga hukumar, yayin da za a sanya kayan aikin da zarar an kammala inganta asibitin.

 

Kwamishinan ta ba da tabbacin cewa Konturola na ma’aikatar a shirye yake a karkashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal, don yin hadin gwiwa da Hukumar Kula da Lafiya don inganta harkar kiwon lafiya.

 

Ta kara da cewa hadin gwiwar za ta hada da tallafin fasaha don gyare-gyare, inganta kayan aiki, da tsarin shiga NHIS.

 

 

 

REL/AMINU DALHATU

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gyaran Hali Zamfara kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

“Kusan kullum muna cikin tashin hankali a Shinkafi,” in ji shi.

Mutumin ya kuma zargi gwamnati daga matakin tarayya har zuwa ƙaramar hukuma da zuba wa matsalar ido.

“Hare-haren suna ci gaba a Birnin Yero, Jangeru, Shanawa, da Shinkafi kanta. Ko jiya da safe sun kawo hari sun kama manoma.”

A cewarsa, manoma da dama sun daina zuwa gonakinsu saboda tsoron za a sace su. Wasu kuma suna zuwa da dare ne kawai don samun ɗan abin da za su ci.

Sai dai, gwamnatin Jihar Zamfara ta ce tana sane da matsalar da jama’ar yankin ke fuskanta, kuma tana ɗaukar matakai don magance ta.

Mai magana da yawun gwamna, Mustafa Jafaru Kaura, ya ce: “Gwamnati tana yin duk abin da ya dace domin ta sharewa jama’a hawaye. Yanzu ma an ba jami’an tsaro da shugabannin ƙananan hukumomi umarni su ɗauki matakin gaggawa.”

Ya kuma jaddada cewa gwamnati tana samun nasara a yaƙi da ‘yan bindigar, yana mai cewa ban da yankin Shinkafi, lamarin ya ragu sosai a sauran sassan Zamfara.

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankin suna fatan wannan tabbacin ba zai zama irin alƙawuran da aka saba ji a baya ba waɗanda ba su taɓa kawo canji mai ma’ana ga rayuwarsu ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara October 15, 2025 Manyan Labarai Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima October 15, 2025 Manyan Labarai Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Aikin Tsaftace Unguwar Kwankwasiyya Mataki Na biyu
  • An Bukaci Manoman Kano Su Shiga Baje Kolin Kayan Noma Na Kasa
  • Gwamna Inuwa ya naɗa sabbin shugabanni a ma’aikatar lafiya ta Gombe
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano