Leadership News Hausa:
2025-12-02@00:40:26 GMT

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Published: 17th, October 2025 GMT

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Sanarwar ta ce: “Sauya wurin da aka yi wa fursuna Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa daya daga cikin cibiyoyin tsarewa da ke karkashin ikon tarayya hanya ce ta gudanar da aiki ta yau da kullum wacce aka yi bisa ga dokokin aiki da ka’idojin hukumar.”

 

Ta kara da bayanin cewa motsa fursunoni daga cibiyar tsarewa zuwa wata musamman wadanda ke da matakan tsaro daban-daban na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora wa hukumar domin tabbatar da ingantaccen tafiyar da fursunoni, gyarawa da kuma dawo da su kan turba.

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Canjawa ko sauya wurin fursuna zuwa wata cibiyar gyaran hali mai matakin tsaro daban da wacce ake tsare da shi a baya na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba Hukumar Kula da Gidajen Yari, kamar yadda Dokar Hukumar ta 2019 ta tanada.”

 

Sanarwar ta ce: “Ana yanke irin wadannan shawara ne bisa la’akari da abubuwa da dama, ciki har da tsaro, tsarin rarraba fursunoni, samun wurin da ya dace a cibiyoyi, da kuma bukatun gyarawa da farfado da fursuna.”

 

CSC Musbahu ya tabbatar wa jama’a cewa duk da wannan sauya wuri, ana ci gaba da kiyaye dukkan hakkokin Malam Abduljabbar.

 

Ya ce: “An tabbatar wa jama’a cewa walwala da dukkan hakkokin shari’a na Malam Abduljabbar suna nan daram karkashin kariyar doka.”

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Wannan sauya wuri ba ya shafar matsayinsa na shari’a, hakkinsa na daukaka kara ko samun damar tuntubar lauyansa.”

 

Jami’in hulda da jama’a ya sake jaddada kudirin hukumar na tabbatar da tsare fursunoni cikin aminci, gyarawa da farfado da su, domin tabbatar da tsaron jiha da kare rayukan jama’a.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn October 17, 2025 Manyan Labarai Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja October 17, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Sanarwar ta tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%

Hukumar kididdiga ta HKI ta basa sanarwan cewa yawan yahudawa da suke ficewa daga haramtacciyar kasar .

Tashar talabijin ta Almayadeen na kasar Lebanon ta nakalto hukumar na bada labarin cewa a shekara ta 2010 yawan masana wadanda suke da shahadar Jami’a ya karu ha rya kai kashi 46% sannan wannan adadin ya cilla sama a shekara ta 2023 bayan fara yakin tufanul aksa zuwa kashi 60.4 %.

Har’ila yau kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayyana cewa a cikin yan shekarun da suka gabata, yahudawa masu ilmin Jami’a da dama sun bar kasar, saboda yana yaki wanda baya karewa a kasar.

Hukumar kididdiga na HKI a cikin yan kwanakin da suka gabata ta yada rahoto dangane da hijiran yahudawa, musamman daga cikin masu ilmi, wanda ya ga masu shigowa kasar sun ragu matuka a kan wadanda suke ficewa zuwa wasu kasashen duniya don neman inda ake zaman lafiya.

Bisa tsohon tsarin kididdiga na HKI, duk wani bayahude wanda ya share shekara guda a kasashen waje bai shiga HKI ko da nay an kwanaki ba to ana daukarsa a matsayin wanda yayi hijira daga kasar.

Amma a sabon tsarin gwamnatin yahudawan, duk wani bayahude wanda yayi kwanaki 275, wato kasa da shekara guda a kasashen waje, ko da yana zuwa kasar nay an kwanaki za’a lissafa shi daga cikin wadanda suka kaura daga kasar.

Bisa tsohon tsarin mutane dubu 16 suke ficewa daga kasar ba tare da sake dawowa ba, a ko wace shekara. Amma a cikin sabon tsarin an nuna cewa wannan adadin ya karu zuwa mutane dubu 36 a ko wace shekara ne suke ficewa ba tare da sun dawo ba. Daga fara yakinnTufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa yanzu adadin yahudawa masu ilmi, wadanda suka hada da likitoci, inginiyoyi da sauransu ne suka fi ficewa daga kasar don duk inda suka je a duniya zasu sami aikin yi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji December 1, 2025 Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran December 1, 2025 Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Maduro Ya Gargadi Amurka Game Da Hankoron Mamaye Rijiyoyin Mai Na Venezuela December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32