Leadership News Hausa:
2025-10-17@20:48:09 GMT

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Published: 17th, October 2025 GMT

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Sanarwar ta ce: “Sauya wurin da aka yi wa fursuna Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa daya daga cikin cibiyoyin tsarewa da ke karkashin ikon tarayya hanya ce ta gudanar da aiki ta yau da kullum wacce aka yi bisa ga dokokin aiki da ka’idojin hukumar.”

 

Ta kara da bayanin cewa motsa fursunoni daga cibiyar tsarewa zuwa wata musamman wadanda ke da matakan tsaro daban-daban na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora wa hukumar domin tabbatar da ingantaccen tafiyar da fursunoni, gyarawa da kuma dawo da su kan turba.

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Canjawa ko sauya wurin fursuna zuwa wata cibiyar gyaran hali mai matakin tsaro daban da wacce ake tsare da shi a baya na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba Hukumar Kula da Gidajen Yari, kamar yadda Dokar Hukumar ta 2019 ta tanada.”

 

Sanarwar ta ce: “Ana yanke irin wadannan shawara ne bisa la’akari da abubuwa da dama, ciki har da tsaro, tsarin rarraba fursunoni, samun wurin da ya dace a cibiyoyi, da kuma bukatun gyarawa da farfado da fursuna.”

 

CSC Musbahu ya tabbatar wa jama’a cewa duk da wannan sauya wuri, ana ci gaba da kiyaye dukkan hakkokin Malam Abduljabbar.

 

Ya ce: “An tabbatar wa jama’a cewa walwala da dukkan hakkokin shari’a na Malam Abduljabbar suna nan daram karkashin kariyar doka.”

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Wannan sauya wuri ba ya shafar matsayinsa na shari’a, hakkinsa na daukaka kara ko samun damar tuntubar lauyansa.”

 

Jami’in hulda da jama’a ya sake jaddada kudirin hukumar na tabbatar da tsare fursunoni cikin aminci, gyarawa da farfado da su, domin tabbatar da tsaron jiha da kare rayukan jama’a.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn October 17, 2025 Manyan Labarai Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja October 17, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Sanarwar ta tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya ce afuwar shugaban ƙasa ya yi masa, ta ba shi kwarin guiwar yin wata sabuwar tafiyar siyasa.

Ya bayyana cewa ya bar tafiyar Kwankwasiyya ne saboda jagorancinta ya yi watsi da shi lokacin da ya fi bukatrsu.

’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEF

Lawan, wanda ya wakilci mazabar Bagwai/Shanono a Jihar Kano, yana cikin mutane 175 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa afuwa a ranar 9 ga watan Oktoba.

An kama shi a shekarar 2021 bayan samun sa  da laifin karɓar cin hanci a 2012, domin cire sunan wani kamfani daga jerin waɗanda ake zargin suna da hannu wajen tafka almundahana a tallafin man fetur.

Bayan ya kammala zaman gidan yari, an sake shi a watan Oktoban 2024.

Lawan, ya ce wannan ta sauya masa tunani game da siyasa da aminci.

A wata hira da ya yi da BBC Hausa, Lawan, ya bayyana cewa tafiyar Kwankwasiyya ta yi watsi da shi, duk da cewa ya dade yana cikin tafiyar.

“Idan Allah Ya jarabce ka, zai nuna maka waye na gaskiya a cikin abokanka,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa wani muhimmin jagora a tafiyar bai taɓa kira ko yi masa jaje ba lokacin da yake gidan yari ko bayan fitarsa.

“Yanzu shekara ɗaya kenan da fitowa ta, amma bai kira ni ba ko ya ce ‘Allah ya taimake ka ba’,” in ji Lawan.

Lawan ya bayyana cewa a lokacin da yake a gidan yari, ya umarci magoya bayansa su shiga jam’iyyar NNPP a lokacin zaɓen 2023.

Amma yanzu yana ganin jam’iyyar karama ce da burinsa na siyasa.

“Siyasa ya kamata ta zama mai faɗi, amma yanzu NNPP ta yi mini ƙarama,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa yanzu zai mayar da hankali kan siyasar ƙasa baki ɗaya, maimakon yin tafiya a waje guda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
  • Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho
  • Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba
  • Hukumar Kula Da GIdajen Gyaran Hali A Zamfara Ta Neman Shigarda Fursunoni Tsarin Inshorar Lafiya Na NHIS
  • Majalisar Dattawa za ta tantance Amupitan a ranar Alhamis
  • Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali