Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
Published: 17th, October 2025 GMT
Sanarwar ta ce: “Sauya wurin da aka yi wa fursuna Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa daya daga cikin cibiyoyin tsarewa da ke karkashin ikon tarayya hanya ce ta gudanar da aiki ta yau da kullum wacce aka yi bisa ga dokokin aiki da ka’idojin hukumar.”
Ta kara da bayanin cewa motsa fursunoni daga cibiyar tsarewa zuwa wata musamman wadanda ke da matakan tsaro daban-daban na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora wa hukumar domin tabbatar da ingantaccen tafiyar da fursunoni, gyarawa da kuma dawo da su kan turba.
Sanarwar ta kara da cewa: “Canjawa ko sauya wurin fursuna zuwa wata cibiyar gyaran hali mai matakin tsaro daban da wacce ake tsare da shi a baya na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba Hukumar Kula da Gidajen Yari, kamar yadda Dokar Hukumar ta 2019 ta tanada.”
Sanarwar ta ce: “Ana yanke irin wadannan shawara ne bisa la’akari da abubuwa da dama, ciki har da tsaro, tsarin rarraba fursunoni, samun wurin da ya dace a cibiyoyi, da kuma bukatun gyarawa da farfado da fursuna.”
CSC Musbahu ya tabbatar wa jama’a cewa duk da wannan sauya wuri, ana ci gaba da kiyaye dukkan hakkokin Malam Abduljabbar.
Ya ce: “An tabbatar wa jama’a cewa walwala da dukkan hakkokin shari’a na Malam Abduljabbar suna nan daram karkashin kariyar doka.”
Sanarwar ta kara da cewa: “Wannan sauya wuri ba ya shafar matsayinsa na shari’a, hakkinsa na daukaka kara ko samun damar tuntubar lauyansa.”
Jami’in hulda da jama’a ya sake jaddada kudirin hukumar na tabbatar da tsare fursunoni cikin aminci, gyarawa da farfado da su, domin tabbatar da tsaron jiha da kare rayukan jama’a.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Sanarwar ta tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan
Tsohon ɗan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya ce afuwar shugaban ƙasa ya yi masa, ta ba shi kwarin guiwar yin wata sabuwar tafiyar siyasa.
Ya bayyana cewa ya bar tafiyar Kwankwasiyya ne saboda jagorancinta ya yi watsi da shi lokacin da ya fi bukatrsu.
’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEFLawan, wanda ya wakilci mazabar Bagwai/Shanono a Jihar Kano, yana cikin mutane 175 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa afuwa a ranar 9 ga watan Oktoba.
An kama shi a shekarar 2021 bayan samun sa da laifin karɓar cin hanci a 2012, domin cire sunan wani kamfani daga jerin waɗanda ake zargin suna da hannu wajen tafka almundahana a tallafin man fetur.
Bayan ya kammala zaman gidan yari, an sake shi a watan Oktoban 2024.
Lawan, ya ce wannan ta sauya masa tunani game da siyasa da aminci.
A wata hira da ya yi da BBC Hausa, Lawan, ya bayyana cewa tafiyar Kwankwasiyya ta yi watsi da shi, duk da cewa ya dade yana cikin tafiyar.
“Idan Allah Ya jarabce ka, zai nuna maka waye na gaskiya a cikin abokanka,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa wani muhimmin jagora a tafiyar bai taɓa kira ko yi masa jaje ba lokacin da yake gidan yari ko bayan fitarsa.
“Yanzu shekara ɗaya kenan da fitowa ta, amma bai kira ni ba ko ya ce ‘Allah ya taimake ka ba’,” in ji Lawan.
Lawan ya bayyana cewa a lokacin da yake a gidan yari, ya umarci magoya bayansa su shiga jam’iyyar NNPP a lokacin zaɓen 2023.
Amma yanzu yana ganin jam’iyyar karama ce da burinsa na siyasa.
“Siyasa ya kamata ta zama mai faɗi, amma yanzu NNPP ta yi mini ƙarama,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu zai mayar da hankali kan siyasar ƙasa baki ɗaya, maimakon yin tafiya a waje guda.