Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-16@09:42:04 GMT

Isra’ila ta taƙaita shigar da kayan agaji Gaza

Published: 16th, October 2025 GMT

Isra’ila ta taƙaita shigar da kayan agaji Gaza

Hukumomi a Isra’ila sun ce gwamnatin ƙasar ta yanke shawarar taƙaita shigar da kayan agaji zuwa zirin Gaza, sannan za ta ɗan dakata ta buɗe bakin iyakar zirin daga Rafas.

Isra’ila ta ce ta ɗauki wannan matakin ne saboda abin da ta kira jan ƙafa da a cewarta Hamas ke yi wajen mayar da sauran gawarwaki da ke hannunsu.

Zuwa yanzu dai gawarwaki huɗu kawai Hamas ta miƙa, sannan akwai rahotannin da ke cewa ƙungiyar za ta miƙa wasu gawarwakin guda huɗu, amma ta ce nemo gawarwakin na da wahalar gaske.

Shi ma Donald Trump ya yi ƙorafi, inda ya buƙaci Hamas ta mayar da gawarwakin “kamar yadda aka yi alƙawari,” in ji shi.

Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta ce wasu gawarwakin sun ɓace, kuma zai yi wahala a gano su.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu na ƙoƙarin mayar da Najeriya mai jam’iyya ɗaya — ADC

Jam’iyyar ADC ta ce sauya sheƙar da wasu gwamnonin jihohi suka yi zuwa jam’iyya mai mulki ya nuna yadda Shugaba Bola Tinubu, ke ƙoƙarin mayar da Najeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya.

A wata sanarwa da Bolaji Abdullahi, mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, ya fitar, ya ce jam’iyyun adawa ba su damu da abin da ya kira “cin amanar siyasa” da gwamnonin suka yi ba.

Gwamna Inuwa ya naɗa sabbin shugabanni a ma’aikatar lafiya ta Gombe Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda

Ya ce zaɓen 2027 ba zai zama takara tsakanin jam’iyyu kawai ba, sai dai ya zama gwagwarmaya tsakanin talakawan Najeriya da gwamnatin da ta jefa rayuwar talakawa cikin wahala.

Abdullahi, ya bayyana cewa komawar gwamnonin jihohin Enugu da Bayelsa zuwa jam’iyyar APC, ta tabbatar da cewa Shugaba Tinubu, na da niyyar raunana dimokuraɗiyya da jam’iyyun adawa a ƙasar nan.

Ya ƙara da cewa duk da cewar gwamnonin sun koma jam’iyya mai mulki a zahirin gaskiya sun bar jama’arsu ne tare da komawa jam’iyyar da ta gaza ciyar da ƙasa gaba.

A cewar Abdullahi, ’yan Najeriya da dama suna cikin wahala saboda gazawar gwamnatin APC, hauhawar farashin kayan abinci, rashin ayyukan yi, matsalar tsaro, rashin ingantaccen tsarin kiwon lafiya, da cin hanci da rashawa.

Ya ce ’yan Najeriya sun yi tsammanin gwamnonin adawa za su yi tsayin daka su kare jama’a da kawo mafita, amma maimakon haka, wasu daga cikinsu sun shiga jam’iyyar mai mulki saboda son rai.

Abdullahi, ya kuma ce duk da APC na murna da samun waɗancan gwamnoni, ADC da sauran jam’iyyun adawa suna farin ciki saboda yanzu ’yan Najeriya za su iya gane waɗanda za su tsaya domin ceto ƙasar nan.

Ya ƙarƙare da cewa zaɓen 2027 zai zama takara kai-tsaye tsakanin talakawan Najeriya da gwamnatin Shugaba Tinubu ta jam’iyyar APC.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Shari’ar Neman Hukunta Isra’ila Kan Batun Gaza
  • Tinubu na ƙoƙarin mayar da Najeriya mai jam’iyya ɗaya — ADC
  • Isra’ila  Za Ta Sake Kai Hare-hare Idan Ta Karbi Dukkan Mutanenta Da Hamas Ta Kama.
  • Hamas Ta Ce HKI Tana Jinkirta Neman Gawakin Yahudawa A Gaza
  • Iran Ta Yi Allah Wadai Da Kalaman Kin Jinin Iran Da Trump Ya Yi A Majalisar Dokokin Isra’ila                             
  • Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Dirar Mikiya Kan Donald Trump Kan Bai Wa Isra’ila Makamai
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza