Aminiya:
2025-11-14@20:39:24 GMT

Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEF

Published: 15th, October 2025 GMT

Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta zuba jari a fannin kayan aikin wanke hannu da kuma ilimin tsafta.

Asusun ya kuma ce kaso 35 cikin 100 na makarantu ne kawai ke da kayan wanke hannu na asali, yayin da kashi 8 cikin 100 na ’yan Najeriya ne kawai ke iya nuna yadda ake wanke hannu daidai.

Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike

Yayin wata ziyara da aka kai makarantu a Jihar Borno a ranar Laraba, a wani ɓangare na bikin Ranar Wanke Hannu ta Duniya ta shekarar 2025, Shugabar Ofishin UNICEF a Maiduguri, Dr. Marie Marcos, ta ce zuba jari a kayan wanke hannu zai ƙara adadin masu zuwa makaranta, inganta lafiyar al’umma, da kuma ƙara ƙwarewa a wuraren aiki.

A cewarta, yankin Arewa maso Gabas ne ke matsayi na biyu a Najeriya dangane da gidaje da ke da wuraren wanke hannu da ruwa da sabulu.

Marie ta ce, “Duk da cewa kaso 99 cikin 100 na ’yan Najeriya sun san lokacin da ya dace a wanke hannu, kashi 8 cikin 100 ne kawai ke iya nuna yadda ake wanke hannu daidai.

“Kaso 17 cikin 100 na gidaje ne ke da damar samun tsafta na asali. Kaso 35 cikin 100 na makarantu ne ke da kayan wanke hannu da ruwa da sabulu.”

“Arewa maso Gabas na matsayi na biyu a Najeriya dangane da gidaje da ke da wuraren wanke hannu da ruwa da sabulu, duk da cewa adadin ya yi kadan a matakin ƙasa baki ɗaya, wato kaso 22.1 cikin 100,” in ji ta.

Sai dai ta ce UNICEF, ta hannun Gwamnatin Jihar Borno, ta tallafa wajen kafa tsarin wanke hannu a makarantu 50 a faɗin jihar, wanda ke kare kusan ’yan makaranta 20,000 a halin yanzu.

“A Jihar Borno, kaso 14 cikin 100 na gidaje ne ke da kayan wanke hannu da sabulu da ruwa. Kashi 20 cikin 100 na makarantu ne ke da kayan tsafta na asali,” in ji ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: wanke hannu a kayan wanke hannu wanke hannu da ke da kayan a makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya

A kwanakin nan ana samun raguwar kujerun maniyyata aikin Hajji daga Najeriya, abin da ya jawo fargaba ga masu shirin zuwa kasa mai tsarki da kuma masu hidimar su.

A da, Najeriya na samun kujeru sama da dubu casa’in daga gwamnatin Saudiyya, amma cikin shekaru kadan da suka gabata adadin ya ragu zuwa kusan dubu sittin da biyar.

 

Kazalika a yanzu gwamnatin na saudiyya ta bayyana cewa idan har maniyyatan Najeriya basu biya cikakken kudaden hajjin bana ba, to akwai alamun sake rage yawan kujerun zuwa dubu hamsin.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Ƙungiyar ASUU DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma

Ko yaya kara raguwar kujerun maniyyatan Najeriya ke kara tasiri ga Najeriya?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
  • Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya
  • UNICEF da Abokan Hulɗa Sun Kaddamar da Shirin Wayar da Kai Kan Rijistar Haihuwa a Yankin Gwarzo
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Venezuela: Maduro Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tsaron Kasa Mai Cikakkiyar Kariya
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza