Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEF
Published: 15th, October 2025 GMT
Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta zuba jari a fannin kayan aikin wanke hannu da kuma ilimin tsafta.
Asusun ya kuma ce kaso 35 cikin 100 na makarantu ne kawai ke da kayan wanke hannu na asali, yayin da kashi 8 cikin 100 na ’yan Najeriya ne kawai ke iya nuna yadda ake wanke hannu daidai.
Yayin wata ziyara da aka kai makarantu a Jihar Borno a ranar Laraba, a wani ɓangare na bikin Ranar Wanke Hannu ta Duniya ta shekarar 2025, Shugabar Ofishin UNICEF a Maiduguri, Dr. Marie Marcos, ta ce zuba jari a kayan wanke hannu zai ƙara adadin masu zuwa makaranta, inganta lafiyar al’umma, da kuma ƙara ƙwarewa a wuraren aiki.
A cewarta, yankin Arewa maso Gabas ne ke matsayi na biyu a Najeriya dangane da gidaje da ke da wuraren wanke hannu da ruwa da sabulu.
Marie ta ce, “Duk da cewa kaso 99 cikin 100 na ’yan Najeriya sun san lokacin da ya dace a wanke hannu, kashi 8 cikin 100 ne kawai ke iya nuna yadda ake wanke hannu daidai.
“Kaso 17 cikin 100 na gidaje ne ke da damar samun tsafta na asali. Kaso 35 cikin 100 na makarantu ne ke da kayan wanke hannu da ruwa da sabulu.”
“Arewa maso Gabas na matsayi na biyu a Najeriya dangane da gidaje da ke da wuraren wanke hannu da ruwa da sabulu, duk da cewa adadin ya yi kadan a matakin ƙasa baki ɗaya, wato kaso 22.1 cikin 100,” in ji ta.
Sai dai ta ce UNICEF, ta hannun Gwamnatin Jihar Borno, ta tallafa wajen kafa tsarin wanke hannu a makarantu 50 a faɗin jihar, wanda ke kare kusan ’yan makaranta 20,000 a halin yanzu.
“A Jihar Borno, kaso 14 cikin 100 na gidaje ne ke da kayan wanke hannu da sabulu da ruwa. Kashi 20 cikin 100 na makarantu ne ke da kayan tsafta na asali,” in ji ta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: wanke hannu a kayan wanke hannu wanke hannu da ke da kayan a makarantu
এছাড়াও পড়ুন:
Mahalarta Taron ‘Sherm-Sheikh” Sun Rattaba Hannu Akan Yarjejeniyar Zaman Lafiya
Shugabannin kasashen Amurka, Masar,Katar da Turkiya da su ka halarci taron na “ Herm-Sheikh” a kasar Masar sun sanya hannu akan yarjejeniyar tsagaita wutar yaki a Gaza.
A jiya Litinin ne dai aka bude taron na Kasar Masar, wanda kuma ya sami halartar Fira ministan kasar Pakistan da kuma shugaban kasar Faransa.
Da yake gabaatar da jawabi, shugaban kasar Amurka Donald Trump yarjejeniyar ta zaman lafiya ta kunshi bangarori da dama, kuma tana tattare da ka’idojin aiwatar da ita.
Akan gawawwakin fursunonin Isra’ilawa, shugaban kasar ta Amurka ya ce ba a kai ga warwarewa ba baki daya, domin har yanzu ana ci gaba da kokarin gano inda suke.
Shi kuwa mai masaukin baki, Shugaban kasar Masar Abdulfattah al-Sisi, ya bayyana cewa; Yarjejeniyar ta Gaza za ta bude wani sabon shafin zaman lafiya a gabas ta tsakiya. Haka nan kuma ya ce; Kafa wa Falasdinawa kasa zai jaddada zaman lafiya.
Shugaban na kasar Amurka ya kuma ce; kasarsa za ta yi aiki kafada da kafada da Amurka da kuma sauran kawayenta domin sake gina yankin na Gaza.
Shi kuwa Fira ministan kasar Pakistan ya yi maraba da shirin zaman lafiyar da ya kawo karshen yakin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD: Mutane 300,000 Su Ka Gudu Daga Sudan Ta Kudu A 2025 October 14, 2025 Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya October 14, 2025 Larijani: Gagarumar Tarbar Da Aka Yi Wa Fursunonin Falasdinawa Ta Nuna Hakikanin Wanda Ya Sami Nasara October 14, 2025 Hamas Ta Mika Yahudawa 7 Daga Cikin 20 Da ke Hannunta Ga Kungiyar Red Cross October 13, 2025 Iran: Kakabawa Kasa Mai Makwabta 16 Takunkumi Ba Abu Ne Mai Sauki Ba. October 13, 2025 An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 13, 2025 Tehran Ta yi Gargadi Game Da Barazanar Yaduwar Fadan Iyakar Afghanisatan Da Pakistan. October 13, 2025 Kungiyar (ASUU) Ta Sanar Da Shiga Yajin Aikin Gargadi A Kasa Baki Daya . October 13, 2025 Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba October 13, 2025 Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza October 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci