Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan
Published: 15th, October 2025 GMT
Tsohon ɗan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya ce afuwar shugaban ƙasa ya yi masa, ta ba shi kwarin guiwar yin wata sabuwar tafiyar siyasa.
Ya bayyana cewa ya bar tafiyar Kwankwasiyya ne saboda jagorancinta ya yi watsi da shi lokacin da ya fi bukatrsu.
’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEFLawan, wanda ya wakilci mazabar Bagwai/Shanono a Jihar Kano, yana cikin mutane 175 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa afuwa a ranar 9 ga watan Oktoba.
An kama shi a shekarar 2021 bayan samun sa da laifin karɓar cin hanci a 2012, domin cire sunan wani kamfani daga jerin waɗanda ake zargin suna da hannu wajen tafka almundahana a tallafin man fetur.
Bayan ya kammala zaman gidan yari, an sake shi a watan Oktoban 2024.
Lawan, ya ce wannan ta sauya masa tunani game da siyasa da aminci.
A wata hira da ya yi da BBC Hausa, Lawan, ya bayyana cewa tafiyar Kwankwasiyya ta yi watsi da shi, duk da cewa ya dade yana cikin tafiyar.
“Idan Allah Ya jarabce ka, zai nuna maka waye na gaskiya a cikin abokanka,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa wani muhimmin jagora a tafiyar bai taɓa kira ko yi masa jaje ba lokacin da yake gidan yari ko bayan fitarsa.
“Yanzu shekara ɗaya kenan da fitowa ta, amma bai kira ni ba ko ya ce ‘Allah ya taimake ka ba’,” in ji Lawan.
Lawan ya bayyana cewa a lokacin da yake a gidan yari, ya umarci magoya bayansa su shiga jam’iyyar NNPP a lokacin zaɓen 2023.
Amma yanzu yana ganin jam’iyyar karama ce da burinsa na siyasa.
“Siyasa ya kamata ta zama mai faɗi, amma yanzu NNPP ta yi mini ƙarama,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu zai mayar da hankali kan siyasar ƙasa baki ɗaya, maimakon yin tafiya a waje guda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Afuwa Farouk Lawan Gidan Yari Kwankwasiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Madugun ’yan adawar kasar Kenya, Raila Odinga, ya mutu
Jagoran ’yan adawa na kasar Kenya kuma tsohon Firaministan kasar, Raila Odinga, ya mutu yana da shekaru 80 a lokacin da yake karɓar magani a ƙasar Indiya, kamar yadda majiyoyin asibiti da ’yan sanda suka tabbatar a ranar Laraba.
Rahotanni daga Asibitin Devamatha da ke Kerala, kudancin Indiya, sun ce Odinga ya samu bugun zuciya mai tsanani a lokacin da yake yawo da safe kusa da otal ɗinsa a birnin Kochi.
Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗeAn garzaya da shi zuwa asibiti nan take, amma likitoci sun tabbatar da rasuwarsa lokacin da suka isa.
Hukumomin ’yan sanda na Indiya sun ce gogaggen ɗan siyasar yana tare da ’yar uwarsa, ’yarsa, likitan kansa, da jami’an tsaro daga Kenya da India a lokacin da lamarin ya faru.
“An kai shi wani asibiti mai zaman kansa da ke kusa, amma aka tabbatar da rasuwarsa,” in ji Krishnan M, Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda na Ernakulam a jihar Kerala.
Jami’ai daga ofishin Odinga da ke Nairobi su ma sun tabbatar da rasuwarsa, yayin da jaridar India ta Mathrubhumi ta rawaito cewa Odinga yana karɓar magani na musamman a Kochi kan wata cuta da ba a bayyana ba.
Odinga, wanda ake ɗaukarsa a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ’yan siyasa a tarihin Kenya tun bayan samun ’yancin kai, ya taba yin takarar shugabancin ƙasa har sau biyar daga tsakanin 1997 zuwa 2022, amma bai taɓa yin nasara ba.
Duk da rashin nasara, ya ci gaba da kasancewa ginshiƙi a siyasar Kenya da kuma zama alamar gwagwarmayar kafuwar dimokuraɗiyya kawo sauyi da kuma juriya.
Rasuwarsa ta kawo ƙarshen wani zamani a siyasar adawa a Kenya, wanda ya jagoranta tsawon shekaru, kuma ta bar babban gibi na jagoranci gabanin zaɓen kasar na 2027 da ke tafe.
Labarin rasuwar Odinga ya haifar da alhini a faɗin Kenya.
Shugaban ƙasa William Ruto ya ziyarci gidan iyalan Odinga da ke unguwar Karen a Nairobi domin jajanta musu.
Daruruwan magoya bayan marigayin kuma sun taru a wajen gidan, da dama daga cikinsu suna kuka, suna raira waƙoƙin haɗin kai, suna daga rassan itatuwa, alamar gargajiya, yayin da suke jimamin mutuwar mutumin da suka fi sani da “Baba,” lakabi da aka fi kiransa da shi a faɗin ƙasar.
An ci gaba da samun sakonnin ta’aziyya daga ɓangarori daban-daban na siyasa da ma daga ƙasashen waje.
Odinga, ɗan Jaramogi Oginga Odinga, mataimakin shugaban ƙasa na farko a Kenya, ya yi wa ƙasar aiki a matsayin Firaminista daga 2008 zuwa 2013 a ƙarƙashin gwamnatin haɗin gwiwa da aka kafa bayan rikicin zaɓen shugaban ƙasa na 2007.
Ya mutu ya bar matarsa Ida Odinga, ’ya’yansu, da jikokinsu.
Ana sa ran iyalansa za su sanar da shirye-shiryen jana’iza tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Kenya.