Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari
Published: 16th, October 2025 GMT
Yari ya bayyana cewa, matsalar tsaro a Arewa ta samo asali ne daga yadda ake amfani da albarkatun kasa da ke yankin ta hanyar da ba ta dace ba, yana kuma gargadin cewa bai kamata a dora laifi kawai a kan gwamnati ba.
“Kafafen sada zumunta suna shafar kowa mai kudi da talaka. Dole ne a tsara dokoki masu tsauri domin kare al’umma,” in ji shi
Sanata Yari ya jaddada cewa giɓin tattalin arziki tsakanin Arewa da Kudu yana kara faɗaɗa, don haka ya buƙaci al’ummar Arewa da su rungumi aikin yi, kirkire-kirkire da dogaro da kai, maimakon dogaro da taimako daga waje.
Doguwa kuwa ya kara da cewa Majalisar Tarayya tana shirye ta tallafa wa duk wani mataki da zai karfafa hadin kai da kuma inganta dabi’un Musulunci.
Shima Sheikh Ahmad Gumi ya ce wasu kasashe na waje na amfani da rashin tsaro a Arewa ta hanyar yaudarar makiyaya marasa ilimi da tayar da fitina domin samun damar mallakar albarkatun kasa.
Ya bukaci a kara tattaunawa tsakanin mazhabobin Musulunci tare da aiwatar da sauye-sauye da za su daidaita tsakanin dokokin amfani da kafafen sada zumunta da kuma kare ‘yancin fadin albarkacin baki.
Taron ya kammala da yin kiran hadin kai da tattaunawa tsakanin mazhabobi, da kuma karfafa tattalin arziki.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
Kwamandan rundunar ta 6, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yabawa sojojin bisa nuna kwarewa da juriya, inda ya bukace su da su ci gaba da sharar daji har sai an kakkaɓe duk wasu masu aikata laifuka gaba daya a jihar Taraba.
Ya bayyana ci gaba da jajircewar rundunar sojin Nijeriya wajen tabbatar da tsaro da tsaron duk ‘yan kasa masu bin doka da oda, yana mai ba da tabbacin cewa, sojojin za su ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro da al’ummomin yankin domin samun dawwamammen zaman lafiya a jihar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA