Yari ya bayyana cewa, matsalar tsaro a Arewa ta samo asali ne daga yadda ake amfani da albarkatun kasa da ke yankin ta hanyar da ba ta dace ba, yana kuma gargadin cewa bai kamata a dora laifi kawai a kan gwamnati ba.

 

“Kafafen sada zumunta suna shafar kowa mai kudi da talaka. Dole ne a tsara dokoki masu tsauri domin kare al’umma,” in ji shi

 

Sanata Yari ya jaddada cewa giɓin tattalin arziki tsakanin Arewa da Kudu yana kara faɗaɗa, don haka ya buƙaci al’ummar Arewa da su rungumi aikin yi, kirkire-kirkire da dogaro da kai, maimakon dogaro da taimako daga waje.

 

Doguwa kuwa ya kara da cewa Majalisar Tarayya tana shirye ta tallafa wa duk wani mataki da zai karfafa hadin kai da kuma inganta dabi’un Musulunci.

 

Shima Sheikh Ahmad Gumi ya ce wasu kasashe na waje na amfani da rashin tsaro a Arewa ta hanyar yaudarar makiyaya marasa ilimi da tayar da fitina domin samun damar mallakar albarkatun kasa.

 

Ya bukaci a kara tattaunawa tsakanin mazhabobin Musulunci tare da aiwatar da sauye-sauye da za su daidaita tsakanin dokokin amfani da kafafen sada zumunta da kuma kare ‘yancin fadin albarkacin baki.

 

Taron ya kammala da yin kiran hadin kai da tattaunawa tsakanin mazhabobi, da kuma karfafa tattalin arziki.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano October 15, 2025 Labarai Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar October 15, 2025 Labarai Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya  October 15, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Kwamandan rundunar ta 6, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yabawa sojojin bisa nuna kwarewa da juriya, inda ya bukace su da su ci gaba da sharar daji har sai an kakkaɓe duk wasu masu aikata laifuka gaba daya a jihar Taraba.

 

Ya bayyana ci gaba da jajircewar rundunar sojin Nijeriya wajen tabbatar da tsaro da tsaron duk ‘yan kasa masu bin doka da oda, yana mai ba da tabbacin cewa, sojojin za su ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro da al’ummomin yankin domin samun dawwamammen zaman lafiya a jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu October 15, 2025 Manyan Labarai 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa October 15, 2025 Labarai Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
  • Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata
  • Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • An Kara Zaburar Da ‘Yan Arewa Game Da Muhimmancin Mallakar Katin Zabe